Wednesday, 2 April 2025

Matata Ko Uwargijiya?

Ƴa ta Saude ta tambayeni wai shin me yasa nake kiran Matata da Uwargijiya. A lokacin muna gaɓar bakin kududdufin mu na bayan gida ne. Tace mahaifin su Ilhambba haka yake kiran matarsa ba. Sai nayi mata murmushi na jawo kofin shayina ina sha. Na cigaba da murmushi...

Taya zan buɗe wannan labarin? Ko nima ban sani ba. Ni na kasance ma'aikacin gwamnati ne wadda yake da hazaka wajen ganin ya gabatar da aikin sa da tsoron Ubangijin sa. Ta haka na haɗu da Matata, farin ciki na. A take damuwata duk suka kau, lokaci guda naji idan har ban mallaketa ba to zan iya ƙona komai!

Na hadu da Matata ne a wajen cin abinci tayi odar filter kofi, wani kofi ne wadda da ƙauna ake sarrafa shi, wato idan har babu kaunar to bai cika ba. Ni kuma ina shan shayi a can baya. A ranar na hadu da ita na biyu saboda mun taba haduwa tabbas kafin a aikomu nan duniyar. 

Tazo ta zauna a teburin da ke kallo na tana mai kallon tsuntsaye da ke ta kullumboto a gajimare. Rana ta kusa komawa gida inda za take haskawa mijin nata hasken ta. Itama Uwargijiya ce!

Bamu ce wa juna komai ba duk da zuciya ta taso tayi amma sai bakina yaki amincewa. Itama a nata bangaren haka akayi. Sai muka koma zantukan da zuciyoyinmu kaɗai ba tare da magana ba. Ina nufin sai muka kasance masu magana da shirun mu. Ban san dai mai zuciyoyin na mu suka tattauna ba amma tabbas na san sun yi magana. Shiyasa ban mamaki ba da na kuma ganinta washegari a wata dandalin da ake shaye-shayen shayi. Dama ai Ruhikan ma'abota shan shayi a koda yaushe a hade suke. Da sunga juna sai su fara hajijiya. 

A ranar dai mun yi magana. Na ce mata sannu ta ce yawwa. Amma a doron wadannan kalmomin guda biyu mun kamalla duk zantukan da ya kamata muyi— na gama saninta itama haka. Washegari kam sai gidansu. Mukai aure cikin dan kankanin lokaci. Muka zama ma'aurata.

A gurin aiki kam mun samu wata kafar samun kuɗaɗe kuma na ƙi na fada mata gaskiya. An dau lokaci a haka har muka samu Saude. Wacce ta kasance cikon farin ciki na. Na kasance a can sama tare da gajimare saboda tsananin farin ciki. 

A ranar da Matata ta gane harkar da nake yi a ofis, ranar ce mafi duhu a rayuwata domin a lokaci guda na hango mutuwata -idan babu ita. Tace Mani dama abin da kake yi kenan? Tace Mani baka tsoron Allah ne? “Ba haka kake ba shin mune muka saka? To zamu bar maka gidan. ”

Nayi shekaru ina son na bar wannan harkalar, Nayi shekaru ina son na gujewa wannan ɓarnar da nake yi amma na kasa. Na roki Ubangijina ya sa na daina amma na kasa dainawa. Amma da wadannan kalmomin suka fito daga bakinta sai naji komai ya gushe. Ruhina ya zama kamar fanko, babu komai cikinsa sai tsagwaron shiru. A haka nai ta luluwa har na riski abubuwan da ba zana iya bayyanawa anan ba. Ni da Ruhina muka amsa, mukayi ta maimaitawa. “Ke uwargija ce!”

I Matata Uwargijiya ce kuma hakan nake kiranta. Uwargijiya. Amma Saude ba za ta fahimta ba. Hakana masu bi na. Shin ta cancanci hakan. Ni dai na san ta ma so ta fi hakan!


2024

No comments:

Post a Comment

Da Kuma Akwai Wannan Lumanar Da Ba Za A Iya Fasalta Wa Ba

Da akwai wannan lumanar da bawa kan riska yayin da ya tsinci wannan littafin da ya yi shekaru yana nema a wata ƙurya a cikin ma'adanar t...