Showing posts with label Zubabbiyar waƙe. Show all posts
Showing posts with label Zubabbiyar waƙe. Show all posts

Friday, 26 December 2025

Fatana

 

Fatana shi ne a ce, ga ni, ga ki, ni da ke, a cikin madafa muna haɗa shayi. Ki ɗan tsoma ganyen na'a-na’a, ni kuma sai na ɗan watsa kanumfari, ki ɓantari citta ki cilla, ni kuma na ƙyasta mana wuta. Muna zaune muna taɓa taɗi, kina ba ni labarin ƙamshin turaren daren amarci, a haka har ya tafasa, mu juye a tambulan sannan mu dawo mu yi zaune tsakar gidanmu. Ga bishiyu sun mana rumfa, ga sautin ƙoton agwagi ga kukan carar ƴan tsaki, ga magunanmu suna ɗawafi tsakaninmu, sai su wuntsila can sai su mirgina can, kina kallon su kina dariyarki. Ke dai ranki na son mage, ni kuma raina na ƙaunar ki. Rayuwa ce mai sauƙi ni da ke muka shirya, babu tarin burika a cikinta, amma akwai so, akwai ƙauna, akwai aminci, nutsuwa, walwala, nishaɗi, bege, muradi, kewa, ƙulafuci, sannan akwai ni, kuma ke ma akwai ki. 

Wace rayuwa ce za ta kai wannan farin ciki da sururi a zuƙatan masoya? 

Fatana shi ne mu kasance a hakan har abada. Ba tare da mun yi magana ba. Muna kallon ruhikanmu a yayin da ruwan sama ya soma sauka kaɗan-kaɗan, yif, yif, yif. Iska mai cike da ni’ima na ɗan kaɗawa a sannu-a sannu. Mu ci gaba da shan shayinmu. Idan ya ƙare mu shanye na cikin bakunan mu. Ina nufin, ko da yake dai, shi ke nan... To amma kuma mene don kin sumbace ni, mene a ciki don kin sha da ni daga gulbinki ke ma kin tsotsa daga tafkina? Ai so ne ke sa a sumbaci ƙauna. 

Abin nufina, fatana shi ne a ce idan mun ƙare wannan da yamma, a lokacin da rana ta je neman masoyinta, ni da ke, za mu karkaɗa haɗin kofi ɗinmu, mu haɗa ruwan kofi sannan mu haye saman farfajiyar benenmu. Muna masu kallon rana da kyawun launinta, ta ɗan yi ja ta ɗan yi shar, tai fatsi-fatsi, ta yi fes abar ƙayatarwa. 

Fatana, ya kasance ke ɗin ma'abociyar shan shayi ce. Don ni da shayi nake rayuwa. Idan babu shi sai ke to duk ɗaya. Don akwai shayi a saman harshenki. Kanumfari uban ƙamshi  na can haƙarƙarin da ke kusa da gurun wuyarki. Akwai ɗanɗanon ruwan shayi a kowace gaɓarki, kusan duk ganyayyakin shayi a katararki suka turke. Akwai komai a cikinki, wannan laɓɓan da ma harshenki. Zo zauna na ƙwanƙwaɗi shayinki. I, na sani sarai da zafi ai, to ai ke ɗin ce mai zafi. Zazzafar masoyiyata mai tururi! 
Fatana shi ne, idan kika kasance ke ɗin ba ma’abociyar shan shayin ba ce, za ki ba ni dama na shanye ki, bi da bi, gaɓa da gaɓa, a sannu-a sannu. Ina mai lasa, ina kwasar daɗin shayin da ba ya buƙatar kayayyakin shayi. 

Fatana a ce kina karance-karance. Kuma kina iya karance-karance. A ce ga mu nan da safiya, gari ya ɗan fara haske kaɗan, rana ba ta kai ga fitowa ba. A ce ga mu nan a kan kujera, ɗaya a bisan cinyar ɗaya, kina karanta mini daga cikin littafan ruhinki, wai ga ni na sukwano a farin doki, na sha naɗi da amawali, ga alkyabba bisana, hannuna da damin fure. Ke kuma kina tsaye, kin ado kin zayyana, taurari sun fito sun reras suna haskaki, tsuntsaye na rera ƙasidarki, kina dakon jirana na ƙaraso a farin doki na ɗauke ki zuwa birnin.... Ni kada ki ba ni labarin zahiri, sun ciƙa ƙarya da ƙarairayi. So nake ki bani labaran duniyarki waɗanda ba sa taɓa ƙarewa. Ki karanto a yayin da ni kuma na lumshe idanuwana ina mai sauraron wannan muryar taki mafi daɗi fiye da ta sarewa. 

Fatana a ce na san ki zahiri da baɗini, shi ya sa zan so a ce muna kallon junanmu da wata idaniyar can ba wannan ba; wannan idaniyar ta fiye hijabai, ba gani take da kyau ba, wata ran ma fa wai sai na sa tabarau. 

Fatana a kodayaushe, a kullum, safiya da maraice, damina da rani, dare da rana, tsakanin bugun zuciyoyi, tsakanin numfarfashi, tsakanin barci da farke, shi ne: na zama koda moɗar gilashin shan shayinki ne, ko kuma ma shayin ma, yadda zana iya ganin cikinki. Ki haɗiye ni, na shige can cikinki nai zamana abi na. Fatana shi ne a ce na gama saninki. Zahirinki da baɗininki. 

To amma ana ko gama sanin masoyi? 

Alhassan Maibasira
March, 2025

Saturday, 14 June 2025

Matafiyan Tsuntsaye


Akwai mutanen da suka kasance kamar tsuntsaye matafiya; sukan shigo rayuwar mutum lokaci guda — na lokaci ƙalilan. Kamar matafiyan tsuntsaye, sukan yi sheƙarsu a rayuwar mutum su yi ta rera masa waƙoƙi — su warkar da ciwukan zuciyar da ya addabe sa, su gyara masa rayuwarsa. Abubuwan da ba ya yi sai ya fara; idan ya faɗi su tayar da shi, idan ya kuskura hanya su dawo da shi bisa tafarki, idan ya nemi shagala su watsa masa ruwa don ya tashi. Idan ya nemi ya ɓata, su nuna masa hanya, duk ta hanyar waƙoƙinsu, waɗanda suke rerawa a kodayaushe. 

Kamar matafiyin tsuntsu, sai ya yi tafiyarsa ya bar sheƙar a saman bishiyar. Babu kowa dai a kai, amma a duk lokacin da mutum ya ɗaga kansa sama, zai hango gidan wannan tsuntsun da ya sauya masa rayuwa. Ba lallai ya kuma dawowa ba, ya tafi kenan. 

To haka Malam Jamilu ya zame wa rayuwata. A daidai lokacin da na gaza gane ina na dosa, sai ya yada zango a bisa bishiyata, ya yi ta rera mini waƙoƙin adabi, tarihi, da wasullan Hausa. Ya yi ta ciyar dani daga tsirran ƙasar Hausa. Idan na kishingiɗa ya taso ni, yace mini na je na nemo masa ciyayi domin mu tada baƙi. Neman ciyayi kam dama na bani wuya, amma duk da haka bai saduda ba. Akwai fa bishiyu da dama a wannan jejin, amma ni kaɗai ya horar fiye da misali. Ni kaɗai nake jin haka — kusan kowa yana sauraren waƙoƙinsa kuma yakan aike su domin su nemo ciyayin. 

A lokaci ƙalilan, bishiyata ta fara rassa, da kaɗan, da kaɗan furarruka suka fara fitowa. Sai dai an ɗau tsawon lokaci kafin bishiyar ta fara ƴaƴa. Lokacin ya bar shingen mu. Idan ma yana dajin baya kusa damu. Ni kuma saboda wautata sai na mance da shi, na ƙi na biɗesa. Na ƙi na tambayi ƙwari da tsutsosin da ke ƙarƙashin ƙasa ko sun taɓa ganinsa. 

Yau dai bishiyar ta fara ƴaƴa — haka nake tunani. To saidai, ashe ba zai taɓa riskar ƴar bishiyar da ya raina ba da kansa. Yar bishiyata da ya rera wa waƙe, ƴar bishiyar da ya zame wa fitila a cikin duhun dare. Yau ba zai gansu ba, yau ba zai taɓa dawowa bisansu ba. Ya tafi kenan, ashe ba zai kuma dawowa ba. 

Akwai mutanen da suka kasance kamar matafiyan tsuntsaye: sai su haskaka alƙaryar mutane da zatinsu, su yi ta shawagi a bisansu, su ƙayatar da duniyarsu. Sai kuma su tafi, za su dawo? Ƙila.... Wasunsu kuma sun tafi kenan. Sheƙarsu na nan dai, hakana tasirin su ga rayuwar mutanen alƙaryar. 

Irin waɗannan mutane ba sa mutuwa, ko sun mutu da akwai ɓurɓushinsu a jikin kowanne. Da akwai baitukan waƙoƙinsu a dashe a ƙalbin mutane. Da akwai ƙarin harshensu a bakunan mutane. Da akwai garɗin koyarwarsu a dasashi da ma saiwar bishiyoyi. Kogunan alƙaryar kam za su ci gaba da ɗaukar wasulla da baƙaken da suka taɓa suɗaɗowa daga waƙoƙinsu. Irin waɗannan mutane na rayuwa har abada. Irin waɗannan mutane ba sa mutuwa.

Allāh Ka gafarta wa bawanKa; Ya kasance kamar matafiyin tsuntsu ne a ban ƙasa. Kai ne Majiɓincinmu, Kai ne Mai rahama a garemu. RahamarKa ta baɗe ko'ina. RahamarKa na da tasiri akan kowa. Ka sanyaya masa yadda ya sanyaya mana. Ya yi iya nasa ƙoƙarin wajen kula da bayinKa; wajen ciyar da halittarKa; wajen ɗanɗana wa al'ummarKa daga ilimin da Ka tsam masa; Ka sa ya zama mai ƙwanƙwaɗa daga tafkin rahamarKa, don, koda ƴar ɗigo ya samu, ta wadace shi har abada. Allāh Ka gafarta wa Malam Jamilu, mutum ne salihu da bai son fitnu, ka buɗe masa ƙofofin rahamarKa, domin, ya kasance mutum ne mai kyawawan ɗabi'u.

Marigayi Malam Jamilu (d. June 2025)



Friday, 25 April 2025

Kukan Kurciya

Akwai wata kurciya da ke zuwa bakin tagata kullum da safiya. Kukanta mai daɗi ke tayar dani daga barci. Na kan kwashi lokaci mai tsayi ina kallonta, ina sauraran kukanta, ina mai ninkaya cikin duniyar mafarkaina wasu lokutan, har da mafarkanta— idan naci sa'a. A cikin duniyar tata mafarkai ne a jere da burika irin tasu ta dabbobi, kar ka tambaye ni wai ashe suna da mafarkai. Ca akai kai kaɗai ne mai iya yin su? 

Ƴar alkawari. Da hakan nake kiranta. Baiwar Allāh abar kwatance. A duniyar tata akwai ma'adanar rayuwarta ta baya. Nan na leƙa wata rana. Sai na ganni a wani kufayi; kango mai haske abin haskakawa. Na gano iyayen ta da ma ƴanuwanta su su duka a zaune. Bayani ne kan yadda rayuwarsu ta ke kasancewa a wannan duniyar. Mahaifin ne ke magana yanzu; baƙi, ƙaƙkaura, idanunsa ja tamkar na Hasbiya. Ya na riƙe da ƴar sanda, alamar tsufa. 

“Iyayen mu sun shaida mana cewa; an shaida wa iyayen su cewa; kakanninsu sun taɓa riskar wani zamani mai ƙayatarwa. A lokacin babu injina ballantana motoci. Saboda haka akwai bishiyoyi da dama, inda ahalinmu ke rayuwa. Rayuwa ce mai sauki a lokacin; babu ƙara, babu datti, babu shara, babu kiɗa; sannan kuma akwai gida. A kowane lokaci suna iya komawa gida ba tare da sun shiga cikin taskar wasi-wasin kasancewar yana nan ko akasinsa ba. Lokacin fa ba a cire masu bishiyu ba bisa ka'ida ba. Kamar na taɓa jiyo kakana Alto yana cewa lokacin Hausawa ke mulkin ƙasar Hausa ba Fulani ba. Sai dai ban san takamaiman lokacin wani sarki ne ba. Ku faɗa mini yarana: shin rayuwa bata fi sauki a da ba. Yanzu ko da ba a cire bishiyoyin ba, ruwan saman mai ƙarfi da ake yi zai cire shi. Duk saboda halayyar bil'adaman dake zamanin mu.”.                                   

Sai mahaifiyar tai caraf ta ƙara da cewar: 

“Ai ko jiya sai da leda ta sarkafe ƙafafuwan Lami da taje farautar ƙwari. Da ƙyar na samu na iya cirewa. Kalli har yanzu da sauranta a cikin yatsunta. Har sai lokacin da Allah ya yi. Abin da ba su ma ganewa— wato su bil'adaman nan— shi ne: abubuwan nan sun ma fi cutar su. Jiya nake ji, a tagar Mallam Sani, wai ga-baki-ɗaya makwararar Jakara ta toshe, saboda haka, mazauna kusa da ita su kiyaye, kasancewar idan aka yi ruwa mai ƙarfi, za a iya ambaliya. Ko-ko ma zafin nan da ake ta zabgawa, ko mu nan da-ba-dan tsarin hallitar da Ubangiji Ya yi mana ba, ai da wani zancen ake. Kuma duk me yasa hakan? Rashin shuka bishiyoyin da za su ci karo, koma su daɗa, waɗanda ake cirewa, da wasu dalilan can.”

Babban ɗan, wanda ya kasance ma'abocin karance-karancen tarihi, sanye da ɗan madubinsa ya ƙara da cewa: “Kun ga kuwa rayuwa ta fi daɗi a lokacin baya. Ina-ma- ina-ma, zan iya komawa can. Na biye wa tawagar Sarkin Zazzau Muhamman Makau lokacin da aka ci ƙasar sa da yaƙi. Yana tafiya da tawagarsa ina biye masa, har su isa Abu-Ja. Nayi zamana a can. Ina ma a ce a wancan ƙarnin a ka haifemu! Ga bishiyu, ga tsaunika, ga ƙoramai, ga ruwa mai kyau. Rayuwa mai daɗi! Uwa uba, ga tsafta. Gari ƙal-ƙal sai kace Aljanna.”

Shin ya Aljanna take? Ka taɓa zuwa ne?” In ji kurciyata, wacce ta kasance a kishingiɗe a saman tsabar da ke kwance a kangon, kanta na kan fika-fikin mahaifiyarta. Sai na ga duka manyan sun ƙalƙale da dariya. Mahaifiyar ko ta janyo ta, ta lakaci hancinta da nata hancin cikin zallar so. 

Mahaifin ya yi gyarar murya ya na mai cewa: “lokaci ya yi, yanzu ina muka dosa?”. A daidai lokacin sai na jiyo ƙarar injin ‘rum-rum-rum’. Sai muka jiyo ‘dum!’ Mai ƙarfi. Na waiga, kafin na juyo kuma, sai na jiyo “Fap...fap...fap”...

Mahaifiya ke jan gora, mahaifin ke bayan ayarin, Ƴaƴayan na tsakiya. Tafiya suke kamar ba za su tafi ba . Da suka nisa sai duk suka juyo, suna masu kallon gidansu a ƙaro na ƙarshe. “Rrrr”— ƙara ya tsaya cak. Amma bishiyarsu— gidansu— babu. Sun tafi kenan. Har abadan... a-ba-da.

Da na dawo zahiriyya, sai na nitsa a cikin kogon tunani. Abubuwan da suka wakana tamkar a mafarki. Na yi mamaki ƙwarai da ba su lura dani ba. Wai shin ko na mutu ne?... Amma kuma wani abu guda daya kasance yana ta yi min kulumboto a cikin zuciyata; kamar na san wurin ko ma na taɓa rayuwa a inda na riske su. Kamar na san kangon nan. Kamar na san ginin nan. Kai, na ma san su! Da na nitsa sai na fahimci cewar, ai inda ma suke tsaye a nan ɗakina yake. Inda aka yi wa ƴaƴayan huɗuba ai a cikin gidan nan yake. Bishiyar da ma na tsakiyar kangon ne. 

Dabbobi ma, kamar ɗan Adam ba sa mance gida. Dabbar ma tsuntuwa. Tsuntsuwar ma Kurciya. Ashe, shi ya sa, a kullum take tashina daga barci. Kukan da take yi ai tuni take min, magana take min, wa'azi take yi min: “Duk inda halittar Ubangiji zai kai ya kawo ba za ya taɓa mantawa da gida ba. Nan ne gidanmu, ba zan iya mantawa da shi ba.”

Washegari na tashi a makare kasancewar ba ta zo ba. Mai tashina ba ta. Sati yazo ya wuce, wata ya rarrafa a sukwane, shekara ta zo a guje. Lokaci mai tsayi ya ja. Amma kullum da tunanin kurciyata nake tashi daga barci.

 “Baba, lokacin shan shayi yayi” na jiyo ɗan autana Sambo na faɗi. Na tashi, na shirya, na ishe su a ƙarƙashin bishiyar da na dasa shekarun baya— irin wacce na gani ne a mafarkin kurciyata. Kuma a inda na ganta a nan na kuma dasa ta. Ga kujeru, ga shayi, ga iyali, sannan ga Kurtattakina a saman bishiya, suna ta kukan su. “Kukan Kurciya dama ai jawabi ne.” ko ni ne na faɗa, ko Kurtattakin dake saman bishiyar ne, ba na ce ba.

MA. Maibasira

24/04/25





Mamako

     Kamar kullum, Kano ta tashi da zafi—zafin juma’a. Amma maimakon ta ci gaba da taku kamar yadda ta saba, sai ta jirkita daga gwadaben ga...