Showing posts with label Hausa. Show all posts
Showing posts with label Hausa. Show all posts

Saturday, 17 May 2025

Gare Ki

Wannan saƙo ne da na daɗe ina ta dakon sa. Yau shekaru sama da huɗu kenan rabon da na yi tozali dake, amma a kullum ruhina da ke yake tashi daga barci. Ki na nan sarkafe abin ki. Kina yadda kike so rabin rai. Jiya na jiyo a radio a na ta zabga muhawara kan maza masu kuka, sai dai na murmusa kawai. Ba na ce ba ki taɓa ganin kuka na ba. Kin sha ganinsa, tunda tare muka taso. Ranar da aka haifi ni ma ai kin gani. Amma duk ruwan hawayen da kika gani basa ɗauke da ƙunci sannan basu da ɗaci. Kawai dai ruwan hawaye ne. Ina da yaƙinin cewa kin gani a ranar da muka yi bankwana. Kin ga ruwan ƙwalla na. To amma, wasu lokutan idan na tuna da cewa mutanen da ke zagaye da ni da ɗan dama, sai naji akwai yiwuwar ba ki gane ni ba; ina can ƙurya ko kuma ɗaka, ina ɗauke da hankici ne ko tsumma, bana ce ba nima. Ban iya tunawa ba... Yanzu dai zan ƙaddara cewa baki taɓa ganin ruwan hawayena mai ɗauke da: ƙunci, da-na-sani, kewa, bege, da so ba. 

Abin da kuwa ma ba ki sani ba shine, wannan ne lokaci na ƙarshe da irin wannan hawaye ya tsatso daga gulbin idanuwana. A duk lokacin da na ji ƙwalla na kan so na ji ya ya yake. Kamar kullum dai babu komai a cikinsa. Ba shi da bambanci da ruwan sha. Ruwan rijiya. Kai hatta ma garɗinsa babu wasu ta’ajibbai da ke kewaye da shi. Hakan kuwa yasa ma na daina kukan. Saboda na san koda na yi sa, ba ya ɗauke da wannan garɗin. Wannan ɗanɗanon da na taɓa riska.

Sahiba, kin tafi da wani ɓari na rayuwata da babu mahalukin da zai iya kawo madadinsa. Ƙunci wani abu ne mai ɗaci, amma ya zauna a wani lungu a ruhina ya yi min kane-kane. A ɓoye yake mulkinsa, ta hanyar amfani da wasu shauƙin can daban wajen isar da saƙon sa. Misali, yanzu sai na ji farin ciki ya mamaye ni haka kurum, idan ko nai ƙuri, sai na ga ashe ba farin cikin kaɗai nake ba — shi ne kaɗai ya bayyana; akwai wani abu mai duhun launi a can ƙurya a zaune yana mai kallona, yana murmushi tare da gyaɗa kansa. 

Na kan ji wani ƙara a cikin ruhina wasu lokutan, koda na duba, sai na ga tana fitowa ne daga wani saƙo a can cikin ruhina. Ƙarar dai ba ta da ƙara. Shiru ce ma. Kawai tsabagen shiru ne ya sanya ƙarar fitowa. Wato dai a can cikina akwai wani irin rami kamar holoƙo da babu komai a cikinsa sai shiru. Ban ma ziyarar sa saboda tsoro da fargabar abin da zan buɗe na gani. E, ƙwarai, ni matsoraci ne, ban son ziyarar in da zai kai ni kushewa. Har yanzu ina da muradai da burika dana ke fatan cimmawa, watarana. Na san idan na shiga wannan rami kam da matsala. Ina gujewa matsala duk da yake dai ba zana iya guje masa ba, sahiba. Wannan ramin kushewarmu ne, a nan na binne soyayyarmu. A nan nake fata wata rana kurwata zata shige dan ta sadu dake.

Sai dai kuma ina rayuwa tamkar ba kya tare dani; tamkar babu ɓurɓushinki a komai na; tamkar iskar da nake shaƙa iska ce kawai, ba sinadaran hazon ruhinki ba; tamkar zuciyata na ci gaba da bugawa ne ba tare da taimakonki ba; tamkar rayuwata — a yanzu — ba wanzuwa take a doron tunaninki ba. Tamkar ba ki, sai dai kuma akwai ki a komai na, Sahiba. Tamkar ba ki, sai dai a duk sanda na tuna wane ni — mantawa nake wasu lokutan — ina ganin ki a samana kina mai kallona. 

Wannan abun, wani lokaci, na ci min rai ƙwarai amma da zaran na tuna cewa duk abubuwan da na lassafta a baya, kina da tasiri a gare su, kuma gaskiya ne, ke ɗin ce sinadarin rayuwata, sai na ji sanyi a ruhina. Sanyin na zuwa ne daga gun ki sahiba. Ai da ma kece mai sanyaya mini zuciya. 

A duk lokacin da na yi koda tunanin cewa kina nesa dani sai ruhina ya gargaɗe ni, domin wai zunubi ne mai girma faɗin haka. Wai kina kusa dani fiye da kusancin jijiyoyi ga ɗan Adam. Kuma haka ne fa, ko? Tunda dai ina tunawa da ke a duk sakan da duk minti. Barci ne kawai ke hanani tunawa dake, kuma ai wasu lokutan ina mafarkinki: wai gamu a wani dausayi; ni dake, da ƙaunar mu, muna masu kallon ruhikan mu ba tare da magana ba, akwai murmushi a saman fuskar mu sannan akwai alamar cikar aminci a kowannenmu. Ina sonki, sahiba. Ina tsananin kewarki. 

A nan alƙalamina — da na sato — ya ƙare daƙushewa, kin fini sanin iya adadin kewarki da nake yi. Kin fini sanin iya nauyin begenki da ke a ruhina. Kin fini sanin cewa ina sonki. Saboda haka, wannan rubutun duk domin ni na yi shi. Ke fa ba kya buƙatar sa — kina ganin gaskiya a can inda kike, saboda haka, kin fini sani. 


April,2024

Wednesday, 7 May 2025

Taurarin Samani

Taurarin Samani


Ba kasafai nake samun kaina a cikin yanayin kaɗaici ba saboda a duk lokacin da na ɗaga kaina na yi duba zuwa ga samani, akwai ababen da ke fitowa daga duniyar tunanina dake ƙayatar da ni. Akwai so, misali. Ina son sa, ina son na yi ta kallon sa. Haka kurum, ba wai don ina so na kasance tare da shi ba ne, ko kusa — wasu abubuwan ganin su daga nesa ya fi, kuma akwai tazara mai yawa tsakanin duniyar tunanina da ta zahirina. Akwai kuma kyawu. Zan iya cewa kusan duk ababen da ke ƙayatar da ni akwai kyawu a cikinsu. Misali, dubi shayi; dubi turirin da ke ziryowa sama daga moɗar shayi; dubi sinadaransa; dubi guminsa da ke jikin shatin moɗar; dubin zatinsa shi karan-kan-sa; Akwai kyawu a shayi da kominsa!


Akwai kuma tarihi, wanda ya kasance mai kawo mini ziyara duk daƙiƙa. Kusan komai na yi, sai na ga ɓurɓushin tarihi a cikinsa. Ballantana, a duniyar tunanina, inda: zamanin da-da ke artabu da zamanin da, masana fikirar da ke artabu da na yanzu, tutar masarautun Hausawa ke artabu da ta Fulani, Gobirawa ke ci gaba da kawo hare-hare Sakkwato da Zamfara, Katsinawan Maraɗi ke kawo sumame Katsina, Buharin Haɗejiya ke bawa daular Sakkwato wahala, musayen zazzafar rubututtuka tsakanin El-kanemi da Muhammadu Ɓallo ke cigaba da kwaranya, Kanawa ke tarbar Sarkinsu Alu bayan Basasa: shi a saman doki, sanye da fararen kaya, mayaƙa a bayansa — bayansa ma a bayansa. Marubuta ke ci gaba da rubutu ba tare da damuwa da duk wannan ba; Sarkin Musulmin da ke shiga ɗaka ya fara rubuta waƙe bayan ya gama fille kan maƙiya. Matar so, ma'abociyar ilimi, Nana Asma'u da ke ciyar da al'umma gaba ta hanyar koyar da su daga ƙoramar iliminta. 


A duk wannan, sai kuma kaga ababen sun rikiɗe sun zama ayar tambaya: “Shin a wani ƙarni nake a duniyar tunanina? A wani zamani nake? Shin kasancewata a wani ƙarnin na da tasiri kan rayuwata ta yau da kullum ko ƙa-ƙa?”


Tambayoyin sai su rikiɗe su zama wata mata, kyakkyawa mai cikar zati da kamala. Ba ta da ko da lulluɓi amma zatinta ya zame mata lulluɓi. A fuskarta akwai wani tabo baƙi mai kama da ɗigon tawada, tana murmushi kuma ta ɓata rai wasu lokutan, ta kalle ni sai kuma ta yi kamar ba ni. Da na yi ƙuri ina dubanta sai na lura da hannunta akwai zanen tambarin arewa a manne a saman tafukanta. Gefe guda kuma a rigarta — can samanta, kusa da wuyarta, ɗan kasa kaɗan — akwai zanen gidan da babu komai a ciki. A gefenta akwai littafan da babu koda ɗigon tawada ciki. Sannan akwai dokin da ba ta hawa sai dai kullum a yi ta mata ado. 


Sai kuma ta rikiɗe ta zama ni. Kamar ni kamar ba ni ba. Ga ni nan da littafai tuli ina ta nazarin su, ga maguna a gefe na manya-manya masu gashi mai laushi da daɗin taɓawa. Farare dukkaninsu. Ga moɗar shayi ina ta sha ina ta kamfata—na gama sanin tarihi—na kafa tarihi. Ina ta murna sai kuma na fara kuka. Kamar dai yadda akwai tarin alheri ga sani, haka ma akwai nakasu ga yawan sani: ga ni nan a wani tsibiri, a zagaye da ni Teku da Bishiyoyi. Sai hadari ya haɗe lokaci guda daga ko’ina. Ina jin ƙishi ina ta jiran ruwan domin na sha. Sai ɗigo ɗaya ya fito daga gajimaren, yai ta juyi har ya iso duniyar tamu har ya faɗa tekun. Da ina ta murna yanzu kuma na fara kuka. Shin ku faɗa min, na sani ne ko kuma ban sani ba? Saboda duk yadda kuka duba, dole ne na koka — ban ɗanɗana ɗigon ba, ba zan iya sha daga tekun ba. Yanzu dai neman ruwa ya kama ni— ko dai na je nemansa ko kuma na zauna na jiraye ruwan sama. 

Sannan akwai adadin kwanaki da shekaru da na ɗiba a duniya, da yadda ma na yi amfani da su. Guje-gujen da na yi da ma kura-kuran da na tafka. Kuma ban da-na-sanin kurakurai na ko kaɗan. Kallon su ma nake ina murmushi a raina. Ba wai saboda na amfana da su ba ne — e ƙila, tabbas ma na amfana da su — illa don kasancewar su kurakurai shi ya sa na ke murmusawa a gare su. Ni gani na nake a cikinsu; ni a mutum ba a halittar da na ƙera wa kaina ba. Ni a gangariyar mutum mai kuskure. Mutum ajizi. Shi ya sa na ke murmushi, don a kullum suna tuna mini da waye ni idan na zama mai mantuwa— saboda mantuwa halittace da aka yi ta don mu. 

Mantuwa na da tasiri ƙwarai a wannan bigire saboda ni dai ba komai nake iya tunawa ba. Misali, ba zan iya tuna ababen da suka faru da nake shekara 10-15 ba, sai dai ƴan kaɗan daga cikin abubuwan da suka wakana. Na san na yi rashin lafiya a waɗannan shekaru, sannan na nuna hazaƙa kwarai a makaranta. Sannan zan ɗan iya tuna abokaina da wasu abubuwan da suka faru da ni kaina. Waɗannan duk ba su kai kaso goma cikin ɗari daga ciki ba. Mantuwa na da daɗi. Har fuskoki ma ina mantasu, ina manta yadda duniyata ta kasance a baya, ina manta waɗanda suka munana min da ma waɗanda suka taimaka min na tsallaka titi. Waɗanda suka zage ni da ma waɗanda suka yabe ni. Tabbas mantuwa na da daɗi! 

Akwai kuma gulbin tunani da ke cigaba da cika kamar a tsakiyar damuna. Zan iya riskar komai a duniya ta hanyar tunani. Ina shagala ƙwarai a wannan yanayi, duk da yake dai, da tunani nake tunanin, amma hakan ba ya hana ni samun cikakkiyar annashuwa a yayin yinsa. Ina farin ciki ƙwarai a wannan dausayin, ina kasancewa tatil tamkar wanda ya kwana a buge tsabar farin ciki. Ko dai tunanin ne ke bugar da ni ko kuma kasancewar na san ina tunanin ne, ba na ce ba. Misali, zan iya tunanin cewa ni ina tunanin abu kaza da kaza sun faru a gare ni, yayin da nake a mace ko a raye. Tunanin ba sa damuwa da kasancewa ta a mace, su ko a jikinsu. Kawai za su cigaba da tafiya ne bisa tsarin da ruhina — ƙila — ya tsara musu. Hakan kuwa na burge ni matuƙa kuma ina samun biyan buƙata — duk da ba ni ba ne nake tsara su, zuwa suke. Biyan buƙatar kuwa da nake samu ba ya wuce kasancewar ina iya sanin abin da zai wakana da raina ko babu. Hakan na matuƙar ƙayatar da ni. Duk da yake, wasu lokutan, ina jan ragamar tunanin zuwa in da nake so su je — saboda zan iya hakan kuma ina da ikon yi hakan, tunda tunanina ne bana kowa ba! Ina matuƙar son wannan ɓarin na duniyar tunanina. Ban son me ya sa ba, amma ina jin, ƙila, saboda ni ne mai yinsu ba kowa ba. 

Hakazalika, duk a nan duniyar, na kan samu kaina a wani yanayin da ke sani tunano duk abubuwan da suka faru, da waɗanda za su faru, da waɗanda nake so su faru, da waɗanda nake fatan su faru, da waɗanda nake hanƙoron faruwar su, da waɗanda haka kurum suke faruwa. Iya wannan na iya kaini duk wani irin bene na farin ciki da ɗan adam zai iya kintatawa. Idan ma kintacen za ya kai can sama-saman-samaniya ne, to ni ma farin ciki na na wurin, tare da.... 

Ka da ku bi ta zancena, kawai ina labarta muku kaɗan ne daga cikin ababen da ke shigowa duniyata da zaran na ɗaga kayina ko ruhina na kalli sama. Da zaran na kaɗaitu, da zaran yanayin shiru ya riske ni. Shi ya sa nake son barci. Amma fa, hakan ba ya hana ni ƙin shiru, saboda a wasu lokutan — a gaskiya, lokuta masu yawa — nakan riski aminci a wannan yanayi. Shi ya sa nake son shiru. Kuma ina son barci. Kuma ma ina son tunani — saboda suma da hular shiru suke zuwa, matayensu kam da kalabinsa, aworworansa, mayafinsa, murmushinsa, kyawunsa. 

Kai ina son shiru! A halin yanzu ma a can wata ƙasa nake a duniyar tunanina, ina zaune a dandamalin rayuwa ina mai kallonta, a samana akwai bishiyar Ɓaure mai ganyayen koraye da cikar rassa. A gefena akwai moɗar shayi. A can gaba na kam akwai kyakkyawar budurwa mai cikar zati, ni kuwa sai kallonta nake: ina shan shayi, ina ta son shiruna!  


08/05/25


Sunayensu

Eh su, mai sunan su,
A haka aka haife su babu sunayensu?

Lokacin da kuke buƙatar kuriunsu,
Ku ne har mazaɓarsu dan ku tantancesu

Loton nan har hotunan su kuka maka,
A bango saboda kar ya wucesu.

Sai yau ɗin da ba ransu,
Saboda rashin ta ido kuka manta sunayensu?

Ina kuke lokacin da a ka kashe su,
Aka sare su sannan aka ƙona su?

Ina kuke lokacin da suke neman agaji,
Da bakunansu, babu mai kula su?

Ina kuke lokacin da aka ciri ɗaya daga kwata,
Aka wurga shi dan a ƙona su?

Ina kuke lokacin da fatar su yake zagwanyewa,
Ƙuna da raɗaɗin azaba na ta cin su?

Ina kuke lokacin da tsabar azaba,
Ta tayar da gaɓoɓin wasunsu?

Ina kuka ɓoye lokacin da aka fara bin,
Karnukan su da sara a na kashe su?

Ina kuka ɓoye lokacin da suke fitar da,
Hayaki daga bakunansu?

Na ce ku matsiyatan nan, marasa mutuncin nan,Masu ribatar nan, 
Ina kuke lokacin da suka rasa rayinsu?

Yau hawaye ke kwaranya a fuskata,
Zuciyata duk ta cika da raɗaɗi sanadinsu.

Akwai nauyi a ruhina a duk lokacin da na tuna da su,
Ji nake yi tamkar na ma san su.

Ban san sunayen su ba har yanzu ,
Saboda ƴaniskan sunƙi su duba su.

Na dai sanya masu suna,
Akwai Aminu akwai Ilyasu.

Da Ɗalhatu da Haruna,
Ƴan uwan juna na san su.

Ibrahima Halilu, kamili,
Ƙurani da Hadisai yana ta dakon su

Zubairu mai masoyiya zubaida,
Har yau ta kasa kallon bidiyon su.

A kullum hawaye ne ke kwaranya,
Idan har ta tuna da yadda aka ma su.

Sai ta ji kamar ma ana ƙona ta,
Idan ta tuna da soyayyarsu da Alkawarin su.

A zuciyarta wuta ke ta burtsatsowa,
Wutar bege da kewansu.

Shi kenan babu Zubairu,
Ya tafi kenan shi da ma sauransu. 

Na tuna da na cikin tayar nan,
Ɗan farin nan mai suna Harisu.

Na tuna yadda suka masa,
Yana ihu su kuwa suna dariyar su.

Ya na ta ajiyar zuciya,
Su kuwa suna ta muguntarsu.

A duk lokacin nan babu ɗaya daga cikin—
Su ƴan iskan nan da ya zo agajinsu.

Haka aka yi ta yi tsawon awanni,
Mutane fa a ƙasarsu.

Aka yi ta ƙona su ana daɓe su,
Da su da muradansu;

Abubuwan da suka so suyi,
Abubuwan ma da suke kan yi nasu.

Da masu ajiye kuɗi a cikin jaka,
Da masu ajiye shi a asusu.

Kudaɗen da za su saya wa,
Masoyansu balangu da kilishi da su.

Kayan sallah kuwa an tura kuɗi,
Yana nan yana jiransu.

Su zo su sanya sa,
Ashe babu damar ya gan su.

Iyayen da ke tagumi duk yamma,
Saboda kewar rashin ɗansu.

Ƴaƴayen da ke zaune a ƙofa,
Suna ta dakon dawawar ubansu.

Ashe ya tafi kenan,
Sai dai gawarsa za a kawo masu.

Ruhiƙa sun ƙunana,
Zuciyoyi ma da rauninsu.

A kullum da shi za su tashi,
Da safiya har zuwa barcin su.

Ƙunar rashi madauwamiya,
A kullum suna ta dakon su.

Ba fa ma rashin ba ne kaɗai,
Har da ma yadda aka zo gunsu —

Da labarin yadda,
aka daddatse jininsu.

Aka bige su, aka ƙona su,
Aka raunata su.

Akwai ƙunci da ɗacin,
Da ke daskare a wani saƙo nasu.

Haka za suyi ta dakon su,
Har ƙarshen rayuwarsu.

Mafarkai da burikan masoyansu,
Na can ƙuryar ruhikansu.

Soyayya da ƙunar rashin masoyansu,
Saboda tsabagen wauta ta mutanen ƙasarsu.

Wautar da ƴaniskan suke rurawa,
Domin biyan buƙata nasu.

Tashin tashina za ta cigaba da ɗorewa,
Har sai sun shiga taitaiyinsu.

Idan suka ƙi shiga ta lalama,
Ai sai a koya masu.

Ta hanyar fitar da su,
daga ɗakin da suke, su je can masu.

Mu koresu, 
Mu yi fatali da kayan su.

Mu ƙi yarda da duk batun su,
Ko ma wani abu da zai fito daga bakunansu.

Mu tsaya da kafar mu,
Wajen yin ball da su.

Tun da sun iya rura wutar kabilanci,
Mu Kore su, mu kakkaɓe tabarmarsu.

Mu faɗa masu ba su da matsuguni a nan,
Su tashi su yi tafiyar su.

Mu faɗa masu ƙasar ta mu,
Ba ta zamowa filin wasansu.

Da zasu dinga amfani damu,
Wajen biyan buƙatarsu.

Mu tuna masu da dubunnai,
Da aka salwantar da ransu.

Mu tuna masu da masoya biyun nan,
Da aka raba su har da soyayyarsu.

Mu tuna masu da hawayen mahaifiyar nan,
Da tagumin ƴaƴayansu.

Mu tuna masu da kwantacciyar ciwon nan,
Da ke binne a zuciyar ahalinsu.

Mu tuna masu da zaluncinsu,
Da ke rura wutar ƙiyayya duk domin su.

Mu tuna masu da soyayyar da ba a kai ga cimmawa ba,
Ƙaunar da aka rusa wa wasunsu.

Mu tuna masu da komai,
Komai har da furfurar wasunsu.

Kar mu bar su,
Kar mu sake su.

Idan suna guduwa,
Mu taɗe su, mu ingiza su!

Su rasa sukuni a yankin su,
Har sai sun tuna da sunayensu.

Sunday, 27 April 2025

Wani abu mai kama da tattaunawa tare da wani ‘Matashi’

Wannan tattaunawa ce da ba ta da mafari, kamar yadda tattaunawar yau da kullum take. Ba wai ba ta da mafari ba ne a haƙiƙanin ta, kawai dai. Kawai dai...

Bayan na tsakuro daga cikin wani rubutu na, wannan ‘matashi(n)’ wanda nake ji kamar ni ne, sai dai, ba ni ɗin bane, cikin tasa hikimar, ya suɗaɗo da tasa mahangar har ya zamana mun ta hangawa junanmu abubuwan da bamu san da akwai su a ruhi kanmu ba. Sunan wannan Matashin Mujahid Yusuf (Matashi). Ga yadda wannan abu mai kama da tattaunawa ya kaya:

Mujahid: 

“Wannan rayuwa haka sai ka ce ba a duniya ba!

Ko da yake da ma, wani shiryayyen mafarki ne da yake abin yiwuwa kaɗai a alam ɗin mafarki. Wannan wani bankaɗar sirrin zuciya ne, wani tonon sililin binne-binnen da zuciya ta rufe na muradi ne.

Abin birgewa, abun kuma tambaya, shin mutane yanzu na samin alaƙantuwa da ababan da ke kewaye da su? Misalin sautin tsallen tsomuwar ganye cikin kofin shayi?”

Ni:

Komai mai yiwuwa ne a duniyar mafarkai. Ba abin da mutum ba zai iya wassafta wa ba. Ba abin da mutum ba zai iya tunanowa ba. Babu kogin mafarkan da mutum ba zai iya afkawa ba. Babu gajimaren da, in ya so, ba zai iya keta wa ba. 

Duniyar mafarki kenan, babu wani abin da ka iya kawo masa cikas. Babu Ubangiji, sai wanda ka ƙera wa kanka. Babu addini, sai wanda ka tufata kanka da shi. Duk da yake Ubangijin ne ya halicce ta, sai ya zama Bai sanya ma ta bango ba. Ma'ana dai, bata da iyaka. Amma ka ga tamu duniyar da iyaka ai. Akwai abubuwan da za mu iya yi, akwai kuma waɗanda ba za mu iya ba, akwai waɗanda sai mun yi da gaske sannan mu iya ma. 

Ashe ma iya cewa kenan, duk wata iriyar soyayya ko ma wani yanayin da kaso, duk za ka riske su a duniyar mafarki, saboda ba ta da iyaka.

Babu abin da mutum ba zai iya alaƙantuwa da shi/ita ba. Har ma akwai abubban da wasu suka ma fi alaƙantuwa da shi fiye da komai. Wasu za kaga motsin bishiyu ne. Wasu kuma motsin busassun ganyayyakin da ke ƙarƙashin bishiyun ne.

Akwai bambanci tsakanin abin da mutum ya wassafta da abin da ya rubuta. Duk inda marubuci ya kai wajen sarrafa zuciyarsa da iya rubutu. Akwai wani tasgaro da rubutun yake samu. Ma'ana dai, ba za mu taɓa iya yin daidai abin da ke kogin zuciyoyin mu ba. Sai dai mu kwatanta. 😊”

Mujahid: 

“Haka. Rubutun namu ne ke da iyaka, ko kuwa mu ke da iyaka a rubutun?”

Ni: 

To fa! Ina jin duka biyu ne. Idan muka tsaya muka ɗan duba shi karan-kan-sa tsarin rubutun. 

Da farko dai, sai mutum ya yi tunani sannan ya rubuta. Tsakanin tunanin da rubutun akwai kalmomin da ka iya suɓucewa. Akwai sakin layin da ka iya maƙalewa a wani saƙon ƙwalwar mu. 

To kuma idan ma muka fara rubutun, mu kan mu, muna sane da wasu wuraren da baza mu so mu taɓa ba, ƙila saboda tasirin Al'adu, Addini, ko ma tsarin ɗan Adam na sa. 

Saboda haka, ko da rubutun ya zo saman alkalamin mu, mu kan daƙushe alƙalamin ruhin mu da kaɗan, domin dai mu samu damar rubutun ba tare da waɗannan abubuwan da ba ma ra'ayi ba.”

Mujahid: 

“Kalmominka sun nuna, ko da ba haka ka nufa ba, cewa mu ke da iyaka a rubutun bisa ababan da ka jero na al'adu, addini da sauransu.

A mahanga ta adabi wannan kam naƙasu ne ga rubutu domin shi adabi ba shi da ɗayan abubuwan da ka lissafo. Sukan ce, kamar mazubin kwalba ne.

A ma'aunin mu'amalantar ɗan adam kuwa, wannan daidai ne. Kuma shi ya fi daidai da fahimtar Addinin Islama. Shi ya sa Yusufun Nabahani yake cewa, ‘Ai ba duk abin da aka sani ne ake faɗa ba.’ Wannan a babin ilimi ma ke nan da yake abin dogaro, balle kuma a babin ƙirƙira.”

Ni: 

“A ƙarshe dole hankali ya yi tasiri ga rubutu; ko muna so, ko ba ma so.”

Godiya mai tarin yawa ga Mallaminmu Mujahid! 


27/04/25

Friday, 25 April 2025

Kukan Kurciya

Akwai wata kurciya da ke zuwa bakin tagata kullum da safiya. Kukanta mai daɗi ke tayar dani daga barci. Na kan kwashi lokaci mai tsayi ina kallonta, ina sauraran kukanta, ina mai ninkaya cikin duniyar mafarkaina wasu lokutan, har da mafarkanta— idan naci sa'a. A cikin duniyar tata mafarkai ne a jere da burika irin tasu ta dabbobi, kar ka tambaye ni wai ashe suna da mafarkai. Ca akai kai kaɗai ne mai iya yin su? 

Ƴar alkawari. Da hakan nake kiranta. Baiwar Allāh abar kwatance. A duniyar tata akwai ma'adanar rayuwarta ta baya. Nan na leƙa wata rana. Sai na ganni a wani kufayi; kango mai haske abin haskakawa. Na gano iyayen ta da ma ƴanuwanta su su duka a zaune. Bayani ne kan yadda rayuwarsu ta ke kasancewa a wannan duniyar. Mahaifin ne ke magana yanzu; baƙi, ƙaƙkaura, idanunsa ja tamkar na Hasbiya. Ya na riƙe da ƴar sanda, alamar tsufa. 

“Iyayen mu sun shaida mana cewa; an shaida wa iyayen su cewa; kakanninsu sun taɓa riskar wani zamani mai ƙayatarwa. A lokacin babu injina ballantana motoci. Saboda haka akwai bishiyoyi da dama, inda ahalinmu ke rayuwa. Rayuwa ce mai sauki a lokacin; babu ƙara, babu datti, babu shara, babu kiɗa; sannan kuma akwai gida. A kowane lokaci suna iya komawa gida ba tare da sun shiga cikin taskar wasi-wasin kasancewar yana nan ko akasinsa ba. Lokacin fa ba a cire masu bishiyu ba bisa ka'ida ba. Kamar na taɓa jiyo kakana Alto yana cewa lokacin Hausawa ke mulkin ƙasar Hausa ba Fulani ba. Sai dai ban san takamaiman lokacin wani sarki ne ba. Ku faɗa mini yarana: shin rayuwa bata fi sauki a da ba. Yanzu ko da ba a cire bishiyoyin ba, ruwan saman mai ƙarfi da ake yi zai cire shi. Duk saboda halayyar bil'adaman dake zamanin mu.”.                                   

Sai mahaifiyar tai caraf ta ƙara da cewar: 

“Ai ko jiya sai da leda ta sarkafe ƙafafuwan Lami da taje farautar ƙwari. Da ƙyar na samu na iya cirewa. Kalli har yanzu da sauranta a cikin yatsunta. Har sai lokacin da Allah ya yi. Abin da ba su ma ganewa— wato su bil'adaman nan— shi ne: abubuwan nan sun ma fi cutar su. Jiya nake ji, a tagar Mallam Sani, wai ga-baki-ɗaya makwararar Jakara ta toshe, saboda haka, mazauna kusa da ita su kiyaye, kasancewar idan aka yi ruwa mai ƙarfi, za a iya ambaliya. Ko-ko ma zafin nan da ake ta zabgawa, ko mu nan da-ba-dan tsarin hallitar da Ubangiji Ya yi mana ba, ai da wani zancen ake. Kuma duk me yasa hakan? Rashin shuka bishiyoyin da za su ci karo, koma su daɗa, waɗanda ake cirewa, da wasu dalilan can.”

Babban ɗan, wanda ya kasance ma'abocin karance-karancen tarihi, sanye da ɗan madubinsa ya ƙara da cewa: “Kun ga kuwa rayuwa ta fi daɗi a lokacin baya. Ina-ma- ina-ma, zan iya komawa can. Na biye wa tawagar Sarkin Zazzau Muhamman Makau lokacin da aka ci ƙasar sa da yaƙi. Yana tafiya da tawagarsa ina biye masa, har su isa Abu-Ja. Nayi zamana a can. Ina ma a ce a wancan ƙarnin a ka haifemu! Ga bishiyu, ga tsaunika, ga ƙoramai, ga ruwa mai kyau. Rayuwa mai daɗi! Uwa uba, ga tsafta. Gari ƙal-ƙal sai kace Aljanna.”

Shin ya Aljanna take? Ka taɓa zuwa ne?” In ji kurciyata, wacce ta kasance a kishingiɗe a saman tsabar da ke kwance a kangon, kanta na kan fika-fikin mahaifiyarta. Sai na ga duka manyan sun ƙalƙale da dariya. Mahaifiyar ko ta janyo ta, ta lakaci hancinta da nata hancin cikin zallar so. 

Mahaifin ya yi gyarar murya ya na mai cewa: “lokaci ya yi, yanzu ina muka dosa?”. A daidai lokacin sai na jiyo ƙarar injin ‘rum-rum-rum’. Sai muka jiyo ‘dum!’ Mai ƙarfi. Na waiga, kafin na juyo kuma, sai na jiyo “Fap...fap...fap”...

Mahaifiya ke jan gora, mahaifin ke bayan ayarin, Ƴaƴayan na tsakiya. Tafiya suke kamar ba za su tafi ba . Da suka nisa sai duk suka juyo, suna masu kallon gidansu a ƙaro na ƙarshe. “Rrrr”— ƙara ya tsaya cak. Amma bishiyarsu— gidansu— babu. Sun tafi kenan. Har abadan... a-ba-da.

Da na dawo zahiriyya, sai na nitsa a cikin kogon tunani. Abubuwan da suka wakana tamkar a mafarki. Na yi mamaki ƙwarai da ba su lura dani ba. Wai shin ko na mutu ne?... Amma kuma wani abu guda daya kasance yana ta yi min kulumboto a cikin zuciyata; kamar na san wurin ko ma na taɓa rayuwa a inda na riske su. Kamar na san kangon nan. Kamar na san ginin nan. Kai, na ma san su! Da na nitsa sai na fahimci cewar, ai inda ma suke tsaye a nan ɗakina yake. Inda aka yi wa ƴaƴayan huɗuba ai a cikin gidan nan yake. Bishiyar da ma na tsakiyar kangon ne. 

Dabbobi ma, kamar ɗan Adam ba sa mance gida. Dabbar ma tsuntuwa. Tsuntsuwar ma Kurciya. Ashe, shi ya sa, a kullum take tashina daga barci. Kukan da take yi ai tuni take min, magana take min, wa'azi take yi min: “Duk inda halittar Ubangiji zai kai ya kawo ba za ya taɓa mantawa da gida ba. Nan ne gidanmu, ba zan iya mantawa da shi ba.”

Washegari na tashi a makare kasancewar ba ta zo ba. Mai tashina ba ta. Sati yazo ya wuce, wata ya rarrafa a sukwane, shekara ta zo a guje. Lokaci mai tsayi ya ja. Amma kullum da tunanin kurciyata nake tashi daga barci.

 “Baba, lokacin shan shayi yayi” na jiyo ɗan autana Sambo na faɗi. Na tashi, na shirya, na ishe su a ƙarƙashin bishiyar da na dasa shekarun baya— irin wacce na gani ne a mafarkin kurciyata. Kuma a inda na ganta a nan na kuma dasa ta. Ga kujeru, ga shayi, ga iyali, sannan ga Kurtattakina a saman bishiya, suna ta kukan su. “Kukan Kurciya dama ai jawabi ne.” ko ni ne na faɗa, ko Kurtattakin dake saman bishiyar ne, ba na ce ba.

MA. Maibasira

24/04/25





Saturday, 22 February 2025

Husufin Farin Ciki: Littafi?


A'a. Husufin Farin Ciki ba littafi ba ne kamar yadda kuke zato — kuka zata. Husufin Farin Ciki ya wuce nan. Matattarar shauƙin bil'adama ne, mafakar ruhikan da suka raunata ne, soron matafiyan da suka rasa guzirin tafiya ne. Gida ne. A'a, ƙasa ce, da ta ƙunshi duk wani al'amurai da ɗan Adam ya taɓa wassafawa a zuciyarsa. Husufin Farin Ciki wani shinge ne da ba a tambayar kyawu ko rashin kyawu, mai ya kamata ko akasinsa. Ba a ma sansu ba ballantana a bambance su. Shigifa ce da duk wanda ya ratsa ta cikinta zai fito mutum kamallale - kamar aƙili, kamar majnuni. Ba wai ana wa mai karatu alkawarin aminci ko nutsuwar zuci ba ne. Ko kusa. Ta yaya za ka riski aminci ba tare da zuciyar ka ta ɗan ragargaje ba. Ta tubure. Ta ɗan haukace ba? To Husufin Farin Ciki hanya ce dan tabbatar da hakan. Tabbas za ka riski abin da kake muradi. Amma... 

Amma kuma sai ya kasance mutum zai iya riskar duk abubuwan da aka lasafta a wata dunƙulalliyar takarda. Shin sai mu kira shi da littafi? Ina! Ya wuce nan. Amma dai littafin ne. Ko-ko nace, dole na yi nazarinsa a mahangar littafi. 

Husufin Farin Ciki diwanin gajerun labarai ne da ke ratsa zuciyoyi tare da tayar da wani irin shauƙin da ba lallai an san da su ba. Labaran na rikiɗewa a yayin da ake karantasu, sai su zama zuma ko maɗaci. Wani zubin kuma sai su gwaraya. Wani zubin ko ka ma gaza bambantasu. Labaran, har wayau, na da ɗanɗano daban-daban. Amma dukansu sun yi tarayya a abu guda. Wato ɗanɗanon ruwa gare su. I, ruwa ba shi da ɗanɗano amma  ai wasu ruwan na da. Wasu lokutan sai mutum ya fara jin ɗanɗanon gishiri wasu lokutan kuma sai labaran su zama kamar ruwan dai. Kamar ruwan sha; marar ɗanɗano; marar ƙamshi. Ɗanɗanon gishiri dai na kama da ruwan teku. Kuma gishiri ma sinadarin hawaye da hauhawar zuci ne. Akwai gishiri a teku sannan akwai shi a ruwan hawaye. Sai dai kuma ba iya ɗanɗanon da mutum zai ji ba kenan. A farko ma ba lallai ya ji komai ba, Kamar dai ruwa. Daga bisani sai ruwan ya rikiɗe ya zama mai gishiri-gishiri. Teku-teku. Kamar dai ruwa, kamar teku.
 
Wasu labaran kam an masu ado ne da alkyabba mai duhun launi. Kamar dai duhun kafin fitowar alfijiri. Wannan alkyabba kuwa tuni yake yi wa makaranta kan: soyayya, ƙauna, bege, rashi, takaici, kewa, rashin rabo, samu, farin ciki, baƙin ciki, jan ciki, harma da ƙoriyar ciki!
 
Wani abun yabawa game da littafin shine yadda a duk sanda mutum zai karanta shi — koda ya taɓa karantawa — zai ji kamar bai ma taɓa karantawa ba. Shauƙin na canzawa ne a koda yaushe. Kamar yadda dai Zuciyar ɗan  Adam yake. A kullum labaran sababbi suke ga makarantansu. Wannan ko ba zai rasa nasaba da sana'ar marubucin ba — Tsafi. Ƙasurgumin matsafi ne. Ya ƙware wajen dabo da kalamai har ma ya busa masu rai. Ya zamana muna ganin su a yayin da muke karanta su. A zahiri kaɗai ne a ke karantawa, a baɗini kam mu ne a labaran muna kallon komai yana gudana a gabanmu. Ba iya busa wa kalamai rai ya yi ba, har shauƙi ya sanya musu. Abin da masana kimiya suka kasa yi, shi wannan BaKanon ya yi da ƴar takarda da alƙalami! 

Wasu labarai ne haka nake ta koɗawa? Kun ma san su, kun taɓa jin su, kun taɓa riskar su. Amma akasarin mutane na kauda kai ga irin waɗannan labaran, ba sa so sam su tuna da su. Mun fi son a kullum mu yi ta rayuwa cikin farin ciki. Babu mai son farin ciki ta yi husufi, to amma kuma ta na yi, a kullum. A kullum labaran duniyar nan dai tamu na da nasu kalar husufin. A layin mu, a unguwar mu, a ƙasar mu. Wannan matsafin ya yi ƙoƙarin kawo mana labaran da ba mu cika son magana akai ba, da wasu kuma waɗanda muka kasance masu kau da kai a kan su. Sai ya hasko mana su, ya nuna mana su, ƙarara
.
Labaran dai sun fi ashirin amma babu waɗanda suka fi ƙayatar da ni sosai kamar: Husufin Farin Ciki, Akwatin Gidan Waya, Dama Dai A Ce, Duniya Labari, Bala da Hannatu, da Tangaraho. Ba wai duka sauran ba su yi bane, ko kusa, duk wanda ya karanta abin da na rubuta a baya ya san dukansu sun yi ainun. Waɗannan ne dai zan ɗan yi tsokaci kaɗan akai domin waɗanda ba su taɓa karantawa ba su ɗan gane mai ya sa nake ta koɗa wannan ‘littafi’. 

Husufin Farin Ciki dai labari ne a cikin Husufin Farin Ciki. Wannan labarin kam ya ci sunansa, domin tun a farko mai karatu zai fara ganin alamar husufi a gajimaren labarin, yana ɗan tuttuɗowa, a hankali. Labarin gabaki ɗaya an rubuta sa ne da alƙalamin rashi mai kama da na kewa, abin mamaki kuwa a kan takardar farin ciki a ka zana labarin (haka nake tunani). Sai dai a lokacin da ake zaton “Husufin Farin Cikin” ya game labarin sai, a hankali, rana ta bayyana, tare da haska labarin, kamar dai yadda take yi wa mazauna duniya. Ai husufi na ɗan ƙanƙanin lokaci ne, zai iya ɗaukar daƙiƙu, mintuna, har shekaru ɗari ma, amma kuma za mu iya neman ranar mu idan muna so. Za mu iya riskar ta, duk da dai alamu ya nuna ta ɓoye ne ba bisa rayin ta ba. “Shin za mu sake samun haihuwa?” Alhaji Ngidda ke nan ke tambayar matarsa jim kaɗan bayan ziyarar husufi. 

Dama Dai A Ce labari ne da ke nuna yanayin al'ummarmu, musamman ta wajen bambance-bambancen mazauna cikinta. Yadda duwatsu suka bambanta; wasu manya, wasu ƙanana; wasu mahaskaka; wasu masu duhu. Yadda ƴan yatsun hannaye suka bambanta a tsayi da yadda ma kaifin rana a duniya ta bambanta sashi-sashi, haka mutanen cikinta suka bambanta. Akwai wasu mutanen da za mu so mu yi tarayya da su, ko da na ƙanƙanin lokaci ne, sai dai kuma idan muka yi duba da abin da ka iya zuwa ya dawo sai mu sauka daga wannan nufi tamu. Ba wai don ba ma son kasancewa tare da su ba ne, sai dai akwai wani abu da muka hango wanda zai iya hana mu aminci nan gaba. Walau ta ita kanta al'ummar mu, ko dai mu karan-kan-mu. Akwai mutanen da zamu so su ainun, amma idan muka yi nazari kan su sai mu ga ba mu dace da su ba. Ba mu ma cancanta da wannan son ba. Sun ɗare mana. Galibi ɗan Adam na kallon duniyar ne da tasa mahangar, kuma ta hakan yake wa duniyar fassara. Amma ita ma duniyar tana kallon kanta ta wata sigar da ba lallai ne mu kula ba. Wannan labarin furen so ne da ke bisa kan bishiyar da hannayenmu ba za su taɓa kaiwa ba. Sai dai zuciyoyin mu su kalla, su adana ta a can wata ƙurya tare da binne ta. Ba tsoro ba ne, a'a, ƙololuwar soyayya ce! 

Bala da Hannatu kuwa mafi gajartar labaran ne. Labari ne wanda muke riskar makamancin sa a rayuwar mu na yau da kullum a wannan sashe na duniyar tamu. Abin da ya fi ƙayatarwa a labarin shi ne gajartar saƙonsa. Kamar dai yadda na ambata ne a baya, cewa mun kasance masu kau da kai ga abubuwa da dama a al'ummar mu. Amma hakan ba shine zai sa matsalar ta kau ba, hakan ma daɗa kambamata yake. Matsalar ta yi ta faɗi da girma a yayin da muka ci gaba da kau da kawunanmu. Rabuwa mai kama da kamuwa; Ba ta da wuri, ba ta da takamaiman lokaci, ba ta da sifa. Faruwa kawai take. Cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kuma. Hannatu ta biɗi Bala da ya sake ta, shi ma ya buɗa bakinsa ya sake ta. Shi ke nan, wannan shafin ya kau. Idan da damar buɗe wani shafin za a yi daga baya. Ƙila Hannatu ta dawo gida ta yi zawarci, ƙila iyayenta su koro ta gida, ƙila su ce mata idan ta bar gidan kar ta dawo gidansu, ƙila ma sun daɗe da tsinke igiyoyin auren, ƙila su zauna a tare a hakan, duk saboda mun kasance al'ummar da ba ta ƙoƙarin warware zarurrukan matsalolinmu, sai dai mu binne matsalar a turɓaya marar ƙarfi, ƙarshe dai matsalolinmu su ci gaba da yaɗuwa ba tare da an magance kowanne ba. Magana mai inganci tare da yin huɓɓasa, a lokacin da ya dace, na iya gyara kaso mai tsoka daga matsalolinmu. Amma ba ma yin hakan a lokacin da ya dace, sai a ƙurarren lokaci, bayan aikin gama ya riga da ya gama. 

Duniya labari, labari ne da ya ɗarsu a zuciyata ya yi min naso. Kamar dai ni ne kowa a ciki kuma kowa ma ni ne. Musamman ga waɗanda suke bibiyar tarihi, irin waɗannan labarai kusan na ko'ina, amma kuma dai a siffar tarihin suke. “Shin wane yare ne kai?” Da a wata sashen duniyar muke da sai mu ce na magabatanmu. Amma a wannan sashen, ba zamu iya faɗar haka ba, domin babu tabaccin cewa daidai muke faɗa. Labarin dai ya ba mu amsar wannan da cewa: “Yare na ne ni.” ”Yare na shine yaren da na tsinci kaina a ciki”. Ba kasafai ake samun irin waɗannan labarai ba a duniyar adabin Hausa. Ƙagaggen Tarihi salo ne da ba kowa ne ke yi ba, saboda yawan binciken da ke tattare da shi. Saboda haka dole a yaba wa wannan marubuci da ya yi ƙoƙarin raya wannan salo na rubutu da ya ke a kushewar adabin Hausa. Labari ne da ya taɓa zamantakewar ƙabilun ƙasar Hausa ta fuskar auratayya, cuɗeɗeniya, narkewa, da adadin zannuwan asali. Musamman yanzu da aka samu wasu masu nuna wane ne BaHausa a ƙasar Hausa, tare da fitar da wasu daga dausayin saboda wasu dalilai na su, wannan labari ya yi ƙoƙarin haska sarƙaƙiyar da ke tattare da asali a ƙasar Hausa ta salon da duk wani makarancin tarihi zai fahimta. Yanzu jikoki da tattaɓa-kunin Inda Musa Hausawa ne ko kuwa Nufawa? Shin sani na da tasiri a asali ko kuwa? Shin kakannin Inda Musa Nufawa ne ko wasu ƙabilun daban? Bayan ƙabilar kakanni, me ke da tasiri a kan asalin mutum? Amsoshin waɗannan tambayoyin na a ɓoye a cikin wannan labari. Idan kana so ka ga yadda ƙasar Hausa take a shekaru ɗari da suka gabata, sai ka zo ka yi iyo a tafkin wannan labari mai ƙamshin duniyar baya!

Akwatin Gidan Waya lula ni ya yi ya tafi da ni wata duniyar can daban, inda nake iya ganin rayuwa a lokaci mabanbanta. Al'adu a lokaci mabanbanta dama mu'amala a lokaci mabanbanta. Labari ne da ya nuna ƙwarewar marubucin a fagen tarihi. Sanin tarihi da iya amfani da shi a labari sai fasihi! Labari ne kan bege da kewa da ma wasu abubuwan. 

Tangaraho labarin soyayya ne; labarin rashi ne; labarin samu ne; labarin zunubi ne; labarin lada ne; labarin ƙauna ne; labarin kewa ne. Labari ne da ba lallai a kuma samun irin sa ba. Kowane harafi, kalma, aya, waƙafi sun yi tarayya ne a waje ɗaya, domin isar da saƙo ɗaya - shiru. Labari ne da ya ginu a kan haka, tun daga farkon har ƙarshen. Shirun fa ba na rashin magana ba ne, ko kaɗan. Shirun da ke cikin ruhika ne aka bayyanar da shi. Irin shirun nan ne da ke sa zuciyoyi su zama kamar fanko, ba komai cikin su sai tsagwaron shiru. Irin wannan shirun ne ya kanannaɗe labarin, har ya kai mun fara ganin kawunanmu a labaran. Ni ne Hajara, ni ne Imrana, ni ne Tangaraho, Ni ce keken Imrana. Labari ne wanda, har wayau, husufi ya ƙwanƙwasa wa ƙofa, sai dai ba iya ƙofar sa ya ƙwanƙwasa ba, har da na ma su karanta shi. Ya samu nasarar ƙutsawa cikin kowane kalma da harafi. Ya yi abin da ya so, in da yaso, mu na so ko ba ma so. Sai dai, wannan Husufin bai zo da wuri ba amma ya wuce da wuri — kamar dai Husufin da aka yi shekarar da ta gabata a duniyar mu. Amma fa bai wuce haka ba, sai da ya bar ɓurbushinsa a iskar da muke shaƙa. Shi ya sa, a yayin da nake rubuta wannan sakin layin, na san na shaƙe sa, kuma iskar da ke ɗauke da shi zuciyata ta shiga. Ga ta can ta yi babakere a cikin zuciyata. Iskokin tangaraho ne suka aiko shi!

A dunƙule dai wannan littafi ya ci sunansa. Sannan marubucin ma ya ci sunansa. Sarrafa zantukan zuci zuwa rubutu sannan a kuma sarrafa su zuwa ababe masu shauƙi, babu shakka sai fasihi. Faɗar abubuwan da muke kauda kai tare da zayyana su ta salo mai ƙayatarwa wani abun a yaba ne. Tabbas marubucin ya ci sunansa. Matsafi ne. Domin ga shi dai duk da na yi nisa da littafin, ga ni a wata duniyar da ya kamata na manta da komi, maimakon haka, na tsinci kaina ina mai tunawa da ham ɗin motar Zainal-Abideen. Ƙarar ham ɗin nake ji. Kuma ƙarar daga cikin zuciyata ne, ba fa ham ɗinsa na farko ba, na ƙarshe. Ham ɗin bankwana.

20/02/25
Alhassan Maibasira

Tuesday, 7 January 2025

Tarihin Muhamman Makau daga bakin Muhamman Makau Kashi na Farko


Shin kun san cikakken sunana? Ba lallai ku sani ba saboda a yadda tsarin ƙasar mu take, suna da laƙabi sun fi tasiri a kan mutum. Ko wanene kuwa. Ko da sarki ne. 
Mutane iri na a ƙasar Hausa basu da yawa gaskiya. Ni mai sarauta ne. Ni sarki ne. Kuma na mulki ƙasa mafi girma da faɗi a kasar Hausa. Ni mai sarauta ne kuma ni sarkin ƙasashe har biyu ne. 
Ni ne Sarkin Zazzau Muhamman Makau ɗan Isyaku Jatau. Sarki na ƙarshe a mulkin Hausa da yayi mulkin ƙasar Zazzau, a birnin Zaria. 
Yanzu na mayar da birni na Abuja. Kun san meye dalili? E to, ci na akai da yaƙi, amma na bazata. Mun je sallar idi a bayan gari domin mu godewa Ubangijin mu a sannan waɗannan Fulanin waɗanda suka ba mahaifina Tuta a baya suka ci garin mu. 
Wai shin mene laifina? Na ƙi na kai caffa, da haraji? Wai ko dai saboda na ɗan sirka musulunci da al'adu kaɗan? Ko dan na dawo da wasu abubuwan da mahaifina ya sa aka daina? Ko dai sun dai samu kafar yaka ta ne dan sun ga mahaifina ya bar duniyar tamu? 
Ni ma ɗin ban sani ba. Na dai san da mahaifina na raye da baza su yi hakan ba. Shin mene laifina?! 
A sanda suka ci garin mu sai mu-yi-mu muka samu damar tserewa; Ni da ƴanuwana da tawagawata da ta saura. Mun tsaya a gundomomi, garuruwa da dama domin su ƙarɓe mu, amma atafau suka ki. Wai suna jin tsoron Fulani. Hahaha! Amma da gaskiyar su, ko nima sun fara bani tsoro. Ji yadda cikin shekaru kaɗan suka cinye ƙasashen hausawa da dama, gashi yau sun zo kaina. To amma, nima baza na raga masu ba, na dai fi son na samu garin da zan zauna ne tukunna kafin mu gwabza dan yanzu a gajiye nake.
Sai da muka nausa can kudancin ƙasar Zazzau a wani gari dake kusa da ƙasar Nupawa (Waɗanda muka taɓa ci da yaki) sannan muka samu masheka. Sai nace wa iyalaina su shiga ciki ni sai naga abinda ya ture wa buzu naɗi yau ɗin nan. Ko ni ko su. 
Hakan kuwa aka yi:
Na yaƙe su, na kashe na kashewa sauran kuma suka tsere, wasunsu sukayi hanyar Lafiyan barebari wasu kuma suka koma birnina, Zaria. 
A sannan ne na yarda na shiga ƙasar da za'a raɗa wa Abuja nan gaba. 
‘Abuja’ dai gari ne mai cike da ƙawa, ga bishiyu ga tsaunika uwa uba ga kuddudufai da dama. Ruwan su kuma ga shi fari ƙal gwanin ban sha'awa ga shi da garɗi da daɗin sha. Shan farko da nayi sai da naji tamkar na bar duniyar! 
Ƙabilu ne ke mulkar garin. Na san su. Suna kawo min caffa akai-akai kuma su ke kula da masu tsaron Yankin. Muna basu tsaro su kuma suna biya mana buƙatun mu na sha'anin mulki. Suna da tsantseni kwarai da gaske ga kuma sannin kimarmu. Muna shiga suka bamu kujerar mulkin su, suka yarje mana mu mulke su da ma ƙasar dake zagaye da su. Suka ce ai ba ƙaramar girmamawa bace a ce kun mayar da wannan garin/ƙasar cibiyar mulkin ku, mun gode. Mun gode. 
A haka muka fara mulkar garin da za a zo a sa wa Abuja...
x


Monday, 6 January 2025

Waƙar Ƙalbi ta Alan Waƙa: Qalbi song Lyrics

Zuciya ta auri tunanina
Babu walwala a Ƙwaƙwalwata 
Hankali ka ceci gaɓoɓi na
Kada zuciya taga bayana
Ga ido yana daga Zucina
Ga ƙafa tana daga Zucina 
Hannuwa suna biye Zucina 
Laffuza suna biye Zucina

Rayuwa akan haka ba shakka bata haifi ɗa da idanu ba

Ya ya zaku min haka gaɓɓai na 
Ku sallamawa ƙalbi na? 
Na gaza da rintse Idanuna
Don saboda saƙar Zucina
Na gaya wa dukka Kaffafuna
Dake biye wa Ƙalbi
Daiman a aikace Ƙalbi na 
ta auri dukka tunani na!

Ilimi suturta jikin Allah kayi mai ado da gaɓaina

Rabbu kar ka bar ni da wayona,
Bazana ɗauka ba.
Ka riƙe gani da tunanina,
Bazana jure ba.
Kada ka sakar wa akalata,
Dan baza na jure ba—
Ji, gani, duƙƙansu tunanina 
Bazan su cetan ba.
Tunda nai riƙo da madubi na,
Baza na taɓe ba.
Annabin da ban ga kamatai ba,
Ba za na sake ba.
Don saboda so da biyar manzo ,
Ka ida dukka muradai na.

Eng: 

Fatana

  Fatana shi ne a ce, ga ni, ga ki, ni da ke, a cikin madafa muna haɗa shayi. Ki ɗan tsoma ganyen na'a-na’a, ni kuma sai na ɗan watsa ka...