Showing posts with label Nigeria. Show all posts
Showing posts with label Nigeria. Show all posts

Wednesday, 7 May 2025

Taurarin Samani

Taurarin Samani


Ba kasafai nake samun kaina a cikin yanayin kaɗaici ba saboda a duk lokacin da na ɗaga kaina na yi duba zuwa ga samani, akwai ababen da ke fitowa daga duniyar tunanina dake ƙayatar da ni. Akwai so, misali. Ina son sa, ina son na yi ta kallon sa. Haka kurum, ba wai don ina so na kasance tare da shi ba ne, ko kusa — wasu abubuwan ganin su daga nesa ya fi, kuma akwai tazara mai yawa tsakanin duniyar tunanina da ta zahirina. Akwai kuma kyawu. Zan iya cewa kusan duk ababen da ke ƙayatar da ni akwai kyawu a cikinsu. Misali, dubi shayi; dubi turirin da ke ziryowa sama daga moɗar shayi; dubi sinadaransa; dubi guminsa da ke jikin shatin moɗar; dubin zatinsa shi karan-kan-sa; Akwai kyawu a shayi da kominsa!


Akwai kuma tarihi, wanda ya kasance mai kawo mini ziyara duk daƙiƙa. Kusan komai na yi, sai na ga ɓurɓushin tarihi a cikinsa. Ballantana, a duniyar tunanina, inda: zamanin da-da ke artabu da zamanin da, masana fikirar da ke artabu da na yanzu, tutar masarautun Hausawa ke artabu da ta Fulani, Gobirawa ke ci gaba da kawo hare-hare Sakkwato da Zamfara, Katsinawan Maraɗi ke kawo sumame Katsina, Buharin Haɗejiya ke bawa daular Sakkwato wahala, musayen zazzafar rubututtuka tsakanin El-kanemi da Muhammadu Ɓallo ke cigaba da kwaranya, Kanawa ke tarbar Sarkinsu Alu bayan Basasa: shi a saman doki, sanye da fararen kaya, mayaƙa a bayansa — bayansa ma a bayansa. Marubuta ke ci gaba da rubutu ba tare da damuwa da duk wannan ba; Sarkin Musulmin da ke shiga ɗaka ya fara rubuta waƙe bayan ya gama fille kan maƙiya. Matar so, ma'abociyar ilimi, Nana Asma'u da ke ciyar da al'umma gaba ta hanyar koyar da su daga ƙoramar iliminta. 


A duk wannan, sai kuma kaga ababen sun rikiɗe sun zama ayar tambaya: “Shin a wani ƙarni nake a duniyar tunanina? A wani zamani nake? Shin kasancewata a wani ƙarnin na da tasiri kan rayuwata ta yau da kullum ko ƙa-ƙa?”


Tambayoyin sai su rikiɗe su zama wata mata, kyakkyawa mai cikar zati da kamala. Ba ta da ko da lulluɓi amma zatinta ya zame mata lulluɓi. A fuskarta akwai wani tabo baƙi mai kama da ɗigon tawada, tana murmushi kuma ta ɓata rai wasu lokutan, ta kalle ni sai kuma ta yi kamar ba ni. Da na yi ƙuri ina dubanta sai na lura da hannunta akwai zanen tambarin arewa a manne a saman tafukanta. Gefe guda kuma a rigarta — can samanta, kusa da wuyarta, ɗan kasa kaɗan — akwai zanen gidan da babu komai a ciki. A gefenta akwai littafan da babu koda ɗigon tawada ciki. Sannan akwai dokin da ba ta hawa sai dai kullum a yi ta mata ado. 


Sai kuma ta rikiɗe ta zama ni. Kamar ni kamar ba ni ba. Ga ni nan da littafai tuli ina ta nazarin su, ga maguna a gefe na manya-manya masu gashi mai laushi da daɗin taɓawa. Farare dukkaninsu. Ga moɗar shayi ina ta sha ina ta kamfata—na gama sanin tarihi—na kafa tarihi. Ina ta murna sai kuma na fara kuka. Kamar dai yadda akwai tarin alheri ga sani, haka ma akwai nakasu ga yawan sani: ga ni nan a wani tsibiri, a zagaye da ni Teku da Bishiyoyi. Sai hadari ya haɗe lokaci guda daga ko’ina. Ina jin ƙishi ina ta jiran ruwan domin na sha. Sai ɗigo ɗaya ya fito daga gajimaren, yai ta juyi har ya iso duniyar tamu har ya faɗa tekun. Da ina ta murna yanzu kuma na fara kuka. Shin ku faɗa min, na sani ne ko kuma ban sani ba? Saboda duk yadda kuka duba, dole ne na koka — ban ɗanɗana ɗigon ba, ba zan iya sha daga tekun ba. Yanzu dai neman ruwa ya kama ni— ko dai na je nemansa ko kuma na zauna na jiraye ruwan sama. 

Sannan akwai adadin kwanaki da shekaru da na ɗiba a duniya, da yadda ma na yi amfani da su. Guje-gujen da na yi da ma kura-kuran da na tafka. Kuma ban da-na-sanin kurakurai na ko kaɗan. Kallon su ma nake ina murmushi a raina. Ba wai saboda na amfana da su ba ne — e ƙila, tabbas ma na amfana da su — illa don kasancewar su kurakurai shi ya sa na ke murmusawa a gare su. Ni gani na nake a cikinsu; ni a mutum ba a halittar da na ƙera wa kaina ba. Ni a gangariyar mutum mai kuskure. Mutum ajizi. Shi ya sa na ke murmushi, don a kullum suna tuna mini da waye ni idan na zama mai mantuwa— saboda mantuwa halittace da aka yi ta don mu. 

Mantuwa na da tasiri ƙwarai a wannan bigire saboda ni dai ba komai nake iya tunawa ba. Misali, ba zan iya tuna ababen da suka faru da nake shekara 10-15 ba, sai dai ƴan kaɗan daga cikin abubuwan da suka wakana. Na san na yi rashin lafiya a waɗannan shekaru, sannan na nuna hazaƙa kwarai a makaranta. Sannan zan ɗan iya tuna abokaina da wasu abubuwan da suka faru da ni kaina. Waɗannan duk ba su kai kaso goma cikin ɗari daga ciki ba. Mantuwa na da daɗi. Har fuskoki ma ina mantasu, ina manta yadda duniyata ta kasance a baya, ina manta waɗanda suka munana min da ma waɗanda suka taimaka min na tsallaka titi. Waɗanda suka zage ni da ma waɗanda suka yabe ni. Tabbas mantuwa na da daɗi! 

Akwai kuma gulbin tunani da ke cigaba da cika kamar a tsakiyar damuna. Zan iya riskar komai a duniya ta hanyar tunani. Ina shagala ƙwarai a wannan yanayi, duk da yake dai, da tunani nake tunanin, amma hakan ba ya hana ni samun cikakkiyar annashuwa a yayin yinsa. Ina farin ciki ƙwarai a wannan dausayin, ina kasancewa tatil tamkar wanda ya kwana a buge tsabar farin ciki. Ko dai tunanin ne ke bugar da ni ko kuma kasancewar na san ina tunanin ne, ba na ce ba. Misali, zan iya tunanin cewa ni ina tunanin abu kaza da kaza sun faru a gare ni, yayin da nake a mace ko a raye. Tunanin ba sa damuwa da kasancewa ta a mace, su ko a jikinsu. Kawai za su cigaba da tafiya ne bisa tsarin da ruhina — ƙila — ya tsara musu. Hakan kuwa na burge ni matuƙa kuma ina samun biyan buƙata — duk da ba ni ba ne nake tsara su, zuwa suke. Biyan buƙatar kuwa da nake samu ba ya wuce kasancewar ina iya sanin abin da zai wakana da raina ko babu. Hakan na matuƙar ƙayatar da ni. Duk da yake, wasu lokutan, ina jan ragamar tunanin zuwa in da nake so su je — saboda zan iya hakan kuma ina da ikon yi hakan, tunda tunanina ne bana kowa ba! Ina matuƙar son wannan ɓarin na duniyar tunanina. Ban son me ya sa ba, amma ina jin, ƙila, saboda ni ne mai yinsu ba kowa ba. 

Hakazalika, duk a nan duniyar, na kan samu kaina a wani yanayin da ke sani tunano duk abubuwan da suka faru, da waɗanda za su faru, da waɗanda nake so su faru, da waɗanda nake fatan su faru, da waɗanda nake hanƙoron faruwar su, da waɗanda haka kurum suke faruwa. Iya wannan na iya kaini duk wani irin bene na farin ciki da ɗan adam zai iya kintatawa. Idan ma kintacen za ya kai can sama-saman-samaniya ne, to ni ma farin ciki na na wurin, tare da.... 

Ka da ku bi ta zancena, kawai ina labarta muku kaɗan ne daga cikin ababen da ke shigowa duniyata da zaran na ɗaga kayina ko ruhina na kalli sama. Da zaran na kaɗaitu, da zaran yanayin shiru ya riske ni. Shi ya sa nake son barci. Amma fa, hakan ba ya hana ni ƙin shiru, saboda a wasu lokutan — a gaskiya, lokuta masu yawa — nakan riski aminci a wannan yanayi. Shi ya sa nake son shiru. Kuma ina son barci. Kuma ma ina son tunani — saboda suma da hular shiru suke zuwa, matayensu kam da kalabinsa, aworworansa, mayafinsa, murmushinsa, kyawunsa. 

Kai ina son shiru! A halin yanzu ma a can wata ƙasa nake a duniyar tunanina, ina zaune a dandamalin rayuwa ina mai kallonta, a samana akwai bishiyar Ɓaure mai ganyayen koraye da cikar rassa. A gefena akwai moɗar shayi. A can gaba na kam akwai kyakkyawar budurwa mai cikar zati, ni kuwa sai kallonta nake: ina shan shayi, ina ta son shiruna!  


08/05/25


Sunayensu

Eh su, mai sunan su,
A haka aka haife su babu sunayensu?

Lokacin da kuke buƙatar kuriunsu,
Ku ne har mazaɓarsu dan ku tantancesu

Loton nan har hotunan su kuka maka,
A bango saboda kar ya wucesu.

Sai yau ɗin da ba ransu,
Saboda rashin ta ido kuka manta sunayensu?

Ina kuke lokacin da a ka kashe su,
Aka sare su sannan aka ƙona su?

Ina kuke lokacin da suke neman agaji,
Da bakunansu, babu mai kula su?

Ina kuke lokacin da aka ciri ɗaya daga kwata,
Aka wurga shi dan a ƙona su?

Ina kuke lokacin da fatar su yake zagwanyewa,
Ƙuna da raɗaɗin azaba na ta cin su?

Ina kuke lokacin da tsabar azaba,
Ta tayar da gaɓoɓin wasunsu?

Ina kuka ɓoye lokacin da aka fara bin,
Karnukan su da sara a na kashe su?

Ina kuka ɓoye lokacin da suke fitar da,
Hayaki daga bakunansu?

Na ce ku matsiyatan nan, marasa mutuncin nan,Masu ribatar nan, 
Ina kuke lokacin da suka rasa rayinsu?

Yau hawaye ke kwaranya a fuskata,
Zuciyata duk ta cika da raɗaɗi sanadinsu.

Akwai nauyi a ruhina a duk lokacin da na tuna da su,
Ji nake yi tamkar na ma san su.

Ban san sunayen su ba har yanzu ,
Saboda ƴaniskan sunƙi su duba su.

Na dai sanya masu suna,
Akwai Aminu akwai Ilyasu.

Da Ɗalhatu da Haruna,
Ƴan uwan juna na san su.

Ibrahima Halilu, kamili,
Ƙurani da Hadisai yana ta dakon su

Zubairu mai masoyiya zubaida,
Har yau ta kasa kallon bidiyon su.

A kullum hawaye ne ke kwaranya,
Idan har ta tuna da yadda aka ma su.

Sai ta ji kamar ma ana ƙona ta,
Idan ta tuna da soyayyarsu da Alkawarin su.

A zuciyarta wuta ke ta burtsatsowa,
Wutar bege da kewansu.

Shi kenan babu Zubairu,
Ya tafi kenan shi da ma sauransu. 

Na tuna da na cikin tayar nan,
Ɗan farin nan mai suna Harisu.

Na tuna yadda suka masa,
Yana ihu su kuwa suna dariyar su.

Ya na ta ajiyar zuciya,
Su kuwa suna ta muguntarsu.

A duk lokacin nan babu ɗaya daga cikin—
Su ƴan iskan nan da ya zo agajinsu.

Haka aka yi ta yi tsawon awanni,
Mutane fa a ƙasarsu.

Aka yi ta ƙona su ana daɓe su,
Da su da muradansu;

Abubuwan da suka so suyi,
Abubuwan ma da suke kan yi nasu.

Da masu ajiye kuɗi a cikin jaka,
Da masu ajiye shi a asusu.

Kudaɗen da za su saya wa,
Masoyansu balangu da kilishi da su.

Kayan sallah kuwa an tura kuɗi,
Yana nan yana jiransu.

Su zo su sanya sa,
Ashe babu damar ya gan su.

Iyayen da ke tagumi duk yamma,
Saboda kewar rashin ɗansu.

Ƴaƴayen da ke zaune a ƙofa,
Suna ta dakon dawawar ubansu.

Ashe ya tafi kenan,
Sai dai gawarsa za a kawo masu.

Ruhiƙa sun ƙunana,
Zuciyoyi ma da rauninsu.

A kullum da shi za su tashi,
Da safiya har zuwa barcin su.

Ƙunar rashi madauwamiya,
A kullum suna ta dakon su.

Ba fa ma rashin ba ne kaɗai,
Har da ma yadda aka zo gunsu —

Da labarin yadda,
aka daddatse jininsu.

Aka bige su, aka ƙona su,
Aka raunata su.

Akwai ƙunci da ɗacin,
Da ke daskare a wani saƙo nasu.

Haka za suyi ta dakon su,
Har ƙarshen rayuwarsu.

Mafarkai da burikan masoyansu,
Na can ƙuryar ruhikansu.

Soyayya da ƙunar rashin masoyansu,
Saboda tsabagen wauta ta mutanen ƙasarsu.

Wautar da ƴaniskan suke rurawa,
Domin biyan buƙata nasu.

Tashin tashina za ta cigaba da ɗorewa,
Har sai sun shiga taitaiyinsu.

Idan suka ƙi shiga ta lalama,
Ai sai a koya masu.

Ta hanyar fitar da su,
daga ɗakin da suke, su je can masu.

Mu koresu, 
Mu yi fatali da kayan su.

Mu ƙi yarda da duk batun su,
Ko ma wani abu da zai fito daga bakunansu.

Mu tsaya da kafar mu,
Wajen yin ball da su.

Tun da sun iya rura wutar kabilanci,
Mu Kore su, mu kakkaɓe tabarmarsu.

Mu faɗa masu ba su da matsuguni a nan,
Su tashi su yi tafiyar su.

Mu faɗa masu ƙasar ta mu,
Ba ta zamowa filin wasansu.

Da zasu dinga amfani damu,
Wajen biyan buƙatarsu.

Mu tuna masu da dubunnai,
Da aka salwantar da ransu.

Mu tuna masu da masoya biyun nan,
Da aka raba su har da soyayyarsu.

Mu tuna masu da hawayen mahaifiyar nan,
Da tagumin ƴaƴayansu.

Mu tuna masu da kwantacciyar ciwon nan,
Da ke binne a zuciyar ahalinsu.

Mu tuna masu da zaluncinsu,
Da ke rura wutar ƙiyayya duk domin su.

Mu tuna masu da soyayyar da ba a kai ga cimmawa ba,
Ƙaunar da aka rusa wa wasunsu.

Mu tuna masu da komai,
Komai har da furfurar wasunsu.

Kar mu bar su,
Kar mu sake su.

Idan suna guduwa,
Mu taɗe su, mu ingiza su!

Su rasa sukuni a yankin su,
Har sai sun tuna da sunayensu.

Mamako

     Kamar kullum, Kano ta tashi da zafi—zafin juma’a. Amma maimakon ta ci gaba da taku kamar yadda ta saba, sai ta jirkita daga gwadaben ga...