Showing posts with label Grief. Show all posts
Showing posts with label Grief. Show all posts

Saturday, 14 June 2025

Matafiyan Tsuntsaye


Akwai mutanen da suka kasance kamar tsuntsaye matafiya; sukan shigo rayuwar mutum lokaci guda — na lokaci ƙalilan. Kamar matafiyan tsuntsaye, sukan yi sheƙarsu a rayuwar mutum su yi ta rera masa waƙoƙi — su warkar da ciwukan zuciyar da ya addabe sa, su gyara masa rayuwarsa. Abubuwan da ba ya yi sai ya fara; idan ya faɗi su tayar da shi, idan ya kuskura hanya su dawo da shi bisa tafarki, idan ya nemi shagala su watsa masa ruwa don ya tashi. Idan ya nemi ya ɓata, su nuna masa hanya, duk ta hanyar waƙoƙinsu, waɗanda suke rerawa a kodayaushe. 

Kamar matafiyin tsuntsu, sai ya yi tafiyarsa ya bar sheƙar a saman bishiyar. Babu kowa dai a kai, amma a duk lokacin da mutum ya ɗaga kansa sama, zai hango gidan wannan tsuntsun da ya sauya masa rayuwa. Ba lallai ya kuma dawowa ba, ya tafi kenan. 

To haka Malam Jamilu ya zame wa rayuwata. A daidai lokacin da na gaza gane ina na dosa, sai ya yada zango a bisa bishiyata, ya yi ta rera mini waƙoƙin adabi, tarihi, da wasullan Hausa. Ya yi ta ciyar dani daga tsirran ƙasar Hausa. Idan na kishingiɗa ya taso ni, yace mini na je na nemo masa ciyayi domin mu tada baƙi. Neman ciyayi kam dama na bani wuya, amma duk da haka bai saduda ba. Akwai fa bishiyu da dama a wannan jejin, amma ni kaɗai ya horar fiye da misali. Ni kaɗai nake jin haka — kusan kowa yana sauraren waƙoƙinsa kuma yakan aike su domin su nemo ciyayin. 

A lokaci ƙalilan, bishiyata ta fara rassa, da kaɗan, da kaɗan furarruka suka fara fitowa. Sai dai an ɗau tsawon lokaci kafin bishiyar ta fara ƴaƴa. Lokacin ya bar shingen mu. Idan ma yana dajin baya kusa damu. Ni kuma saboda wautata sai na mance da shi, na ƙi na biɗesa. Na ƙi na tambayi ƙwari da tsutsosin da ke ƙarƙashin ƙasa ko sun taɓa ganinsa. 

Yau dai bishiyar ta fara ƴaƴa — haka nake tunani. To saidai, ashe ba zai taɓa riskar ƴar bishiyar da ya raina ba da kansa. Yar bishiyata da ya rera wa waƙe, ƴar bishiyar da ya zame wa fitila a cikin duhun dare. Yau ba zai gansu ba, yau ba zai taɓa dawowa bisansu ba. Ya tafi kenan, ashe ba zai kuma dawowa ba. 

Akwai mutanen da suka kasance kamar matafiyan tsuntsaye: sai su haskaka alƙaryar mutane da zatinsu, su yi ta shawagi a bisansu, su ƙayatar da duniyarsu. Sai kuma su tafi, za su dawo? Ƙila.... Wasunsu kuma sun tafi kenan. Sheƙarsu na nan dai, hakana tasirin su ga rayuwar mutanen alƙaryar. 

Irin waɗannan mutane ba sa mutuwa, ko sun mutu da akwai ɓurɓushinsu a jikin kowanne. Da akwai baitukan waƙoƙinsu a dashe a ƙalbin mutane. Da akwai ƙarin harshensu a bakunan mutane. Da akwai garɗin koyarwarsu a dasashi da ma saiwar bishiyoyi. Kogunan alƙaryar kam za su ci gaba da ɗaukar wasulla da baƙaken da suka taɓa suɗaɗowa daga waƙoƙinsu. Irin waɗannan mutane na rayuwa har abada. Irin waɗannan mutane ba sa mutuwa.

Allāh Ka gafarta wa bawanKa; Ya kasance kamar matafiyin tsuntsu ne a ban ƙasa. Kai ne Majiɓincinmu, Kai ne Mai rahama a garemu. RahamarKa ta baɗe ko'ina. RahamarKa na da tasiri akan kowa. Ka sanyaya masa yadda ya sanyaya mana. Ya yi iya nasa ƙoƙarin wajen kula da bayinKa; wajen ciyar da halittarKa; wajen ɗanɗana wa al'ummarKa daga ilimin da Ka tsam masa; Ka sa ya zama mai ƙwanƙwaɗa daga tafkin rahamarKa, don, koda ƴar ɗigo ya samu, ta wadace shi har abada. Allāh Ka gafarta wa Malam Jamilu, mutum ne salihu da bai son fitnu, ka buɗe masa ƙofofin rahamarKa, domin, ya kasance mutum ne mai kyawawan ɗabi'u.

Marigayi Malam Jamilu (d. June 2025)



Saturday, 17 May 2025

Gare Ki

Wannan saƙo ne da na daɗe ina ta dakon sa. Yau shekaru sama da huɗu kenan rabon da na yi tozali dake, amma a kullum ruhina da ke yake tashi daga barci. Ki na nan sarkafe abin ki. Kina yadda kike so rabin rai. Jiya na jiyo a radio a na ta zabga muhawara kan maza masu kuka, sai dai na murmusa kawai. Ba na ce ba ki taɓa ganin kuka na ba. Kin sha ganinsa, tunda tare muka taso. Ranar da aka haifi ni ma ai kin gani. Amma duk ruwan hawayen da kika gani basa ɗauke da ƙunci sannan basu da ɗaci. Kawai dai ruwan hawaye ne. Ina da yaƙinin cewa kin gani a ranar da muka yi bankwana. Kin ga ruwan ƙwalla na. To amma, wasu lokutan idan na tuna da cewa mutanen da ke zagaye da ni da ɗan dama, sai naji akwai yiwuwar ba ki gane ni ba; ina can ƙurya ko kuma ɗaka, ina ɗauke da hankici ne ko tsumma, bana ce ba nima. Ban iya tunawa ba... Yanzu dai zan ƙaddara cewa baki taɓa ganin ruwan hawayena mai ɗauke da: ƙunci, da-na-sani, kewa, bege, da so ba. 

Abin da kuwa ma ba ki sani ba shine, wannan ne lokaci na ƙarshe da irin wannan hawaye ya tsatso daga gulbin idanuwana. A duk lokacin da na ji ƙwalla na kan so na ji ya ya yake. Kamar kullum dai babu komai a cikinsa. Ba shi da bambanci da ruwan sha. Ruwan rijiya. Kai hatta ma garɗinsa babu wasu ta’ajibbai da ke kewaye da shi. Hakan kuwa yasa ma na daina kukan. Saboda na san koda na yi sa, ba ya ɗauke da wannan garɗin. Wannan ɗanɗanon da na taɓa riska.

Sahiba, kin tafi da wani ɓari na rayuwata da babu mahalukin da zai iya kawo madadinsa. Ƙunci wani abu ne mai ɗaci, amma ya zauna a wani lungu a ruhina ya yi min kane-kane. A ɓoye yake mulkinsa, ta hanyar amfani da wasu shauƙin can daban wajen isar da saƙon sa. Misali, yanzu sai na ji farin ciki ya mamaye ni haka kurum, idan ko nai ƙuri, sai na ga ashe ba farin cikin kaɗai nake ba — shi ne kaɗai ya bayyana; akwai wani abu mai duhun launi a can ƙurya a zaune yana mai kallona, yana murmushi tare da gyaɗa kansa. 

Na kan ji wani ƙara a cikin ruhina wasu lokutan, koda na duba, sai na ga tana fitowa ne daga wani saƙo a can cikin ruhina. Ƙarar dai ba ta da ƙara. Shiru ce ma. Kawai tsabagen shiru ne ya sanya ƙarar fitowa. Wato dai a can cikina akwai wani irin rami kamar holoƙo da babu komai a cikinsa sai shiru. Ban ma ziyarar sa saboda tsoro da fargabar abin da zan buɗe na gani. E, ƙwarai, ni matsoraci ne, ban son ziyarar in da zai kai ni kushewa. Har yanzu ina da muradai da burika dana ke fatan cimmawa, watarana. Na san idan na shiga wannan rami kam da matsala. Ina gujewa matsala duk da yake dai ba zana iya guje masa ba, sahiba. Wannan ramin kushewarmu ne, a nan na binne soyayyarmu. A nan nake fata wata rana kurwata zata shige dan ta sadu dake.

Sai dai kuma ina rayuwa tamkar ba kya tare dani; tamkar babu ɓurɓushinki a komai na; tamkar iskar da nake shaƙa iska ce kawai, ba sinadaran hazon ruhinki ba; tamkar zuciyata na ci gaba da bugawa ne ba tare da taimakonki ba; tamkar rayuwata — a yanzu — ba wanzuwa take a doron tunaninki ba. Tamkar ba ki, sai dai kuma akwai ki a komai na, Sahiba. Tamkar ba ki, sai dai a duk sanda na tuna wane ni — mantawa nake wasu lokutan — ina ganin ki a samana kina mai kallona. 

Wannan abun, wani lokaci, na ci min rai ƙwarai amma da zaran na tuna cewa duk abubuwan da na lassafta a baya, kina da tasiri a gare su, kuma gaskiya ne, ke ɗin ce sinadarin rayuwata, sai na ji sanyi a ruhina. Sanyin na zuwa ne daga gun ki sahiba. Ai da ma kece mai sanyaya mini zuciya. 

A duk lokacin da na yi koda tunanin cewa kina nesa dani sai ruhina ya gargaɗe ni, domin wai zunubi ne mai girma faɗin haka. Wai kina kusa dani fiye da kusancin jijiyoyi ga ɗan Adam. Kuma haka ne fa, ko? Tunda dai ina tunawa da ke a duk sakan da duk minti. Barci ne kawai ke hanani tunawa dake, kuma ai wasu lokutan ina mafarkinki: wai gamu a wani dausayi; ni dake, da ƙaunar mu, muna masu kallon ruhikan mu ba tare da magana ba, akwai murmushi a saman fuskar mu sannan akwai alamar cikar aminci a kowannenmu. Ina sonki, sahiba. Ina tsananin kewarki. 

A nan alƙalamina — da na sato — ya ƙare daƙushewa, kin fini sanin iya adadin kewarki da nake yi. Kin fini sanin iya nauyin begenki da ke a ruhina. Kin fini sanin cewa ina sonki. Saboda haka, wannan rubutun duk domin ni na yi shi. Ke fa ba kya buƙatar sa — kina ganin gaskiya a can inda kike, saboda haka, kin fini sani. 


April,2024

Monday, 5 May 2025

Kandalata

From Pinterest
Baza na yabe su ba,
Su waɗannan da suka sace mini kuriciyata.

Baza na je gun su ba,
Su dai masu sace mini dukiyata.

Baza na kula su ba,
Su waɗancan masu zaluntata.

Duk da hakan ba zai hana ni faɗa ba,
Kan yadda suke gudanar da ƙasata.

A yau babu walwala ta zahiri,
Ta tunanin ma babu ita.

Babu sukunin yin barci,
Babu sukunin yin mata.

Abinci ya wahala,
Magidanta sai dai su kwatanta.

Ga su can a ofis,
Suna can suna ribatata.

Suyi ado da ƙawa,
A ce ga Kapasiti suna bazata.

Ƙwalwar su a doɗe,
Ba Arabin, Bokon ma da ƙyar a ka sha ta.

Ba su san komai ba a harkar mulki 
sai dai nuna Bajinta—

Wajen zalunci kan marasa galihu,
Ga ƙasa nan sun ƙi su gyarata.

Komai na ƙasar ya lalace,
Mu kaɗai ya rage su lalata!

Mutum da rigar sa da a cike,
Yau shi ke yawo a cikinta.

A yau ƙiriniya babu ita,
Yara sun dena ta-ta-ta.

Daga sun taso,
Sai dai a jibga masu shirgi dan suje ƙolanta.

Makarantu sun rufeta,
Mallamai duk sun jigata.

Masana'antunmu ma na gida,
Duk an bi an gurgunta.

Dan talaka ba shi ba shinkafa,
Sai dai tsabar da zai iya kwatanta.

Iyaye sai zulumi,
Ƴaƴaye kuwa sai dai su ƙarata.

Dan Babu ma gonar,
Da za su je su nomata.

Idan sun tafi ma,
Babu tabbacin zasu iya komai ma a kanta—

Sai sun biya haraji,
Ko kuwa a ƙonata.

Ƴan bindiga daɗi,
Na cin kariyar su batare da sun babbakata.

Manyan mu na yawo,
Da tsaro domin su tsereta.

Fyaɗe, ƙwace, kisa,
Sun addabi ƙasata.

Har na tuna da wata yarinya,
A can saman tsauni, Kandalata.

Ta kan shigo cikin Gari duk sati 
domin ta sai da furarta.

Da shi ta ke ƙoƙarin,
Ciyar da ahalinta.

Bom ɗin wajen mauludi,
Ya kashe mahaifinta, ya raunata uwarta.

A kullum da ka kalleta,
Sai ka ji zuciyarka ta raunata.

Na tuna da yadda,
Su ƴan iskan suka ishe ta.

Suka kama uwarta,
Ita ma kandala suka kamota.

Suka afka mata—
A gaban uwarta.

Babu ƙwalla ko guda,
Idan ka kalli idaniyarta.

Akwai zulumi da tsana,
A can cikin zuciyarta—

Sun kwanta ruf,
Ita ma hakanta.

Kandalata dake zuwa gaɗa,
Ƴar yarinya ƙarama dake wasanta.

Yau babu ita,
Sai dai ƙoƙonta.

Ta shige cikinta,
Ta yi ruf, ta rufe abinta.

Kandalata da ke son ta zama likita,
Yau da wuya ma kaga fitarta.

Mahaifiyarta ma wacce ta ke gani,
Ta haɗiyi zuciya ta barta.

Yau ƙasar ta da ta ke kishi,
Ta yarda aka hainceta.

Babu wanda ya zo agajinta,
Babu ma mai kallon ta.

Ita kaɗanta,
ke ta dakon kayanta;

Ƙunar rai da,
Azabar zuciyarta.

Ta kan kalli rana,
Da yamma daga tagarta.

Ta kan kwatanta
rayuwarta da ranarta.

Sai dai ita ba ta zuwa ko'ina,
Daga ɗaki sai gadonta.

Ilimi babu shi,
Aikin ma ba ta.

Kandalata ba ta,
Ta ɓace ɓat a duniyarta.

Wannan yarinyar da na sani,
A kullum tana cikin murmushinta.

Yau a halin da take,
Babu ita babu murmushinta.

Ga su can a ofis,
Suna ta harkokinsu babu ita—

A zancen su, da kalaman bakinsu,
Ba sa ko furtata.

Al'ummarmu sun mance da ita,
Kowa ma yayi kamar babu ita.

Kandalata ta rufe ƙofar rayuwarta,
Ta tsani alummarta.

Wani lokacin har tsanar,
Na gangarowa ƙuncinta.

Ta hanyar hawaye,
Da ke zirya a saman fuskarta.

Ta kan tunano rayuwarta—
Ta baya da raunin zuciyarta.

Ta kan tuna da raɗadin da ke,
Binne a birnin zuciyarta—

A duk sakan da minti,
Dake motsi a rayuwarta.

O ni Kandalata!
Labarin ki akwai zafi ƙwarai na hankalta.

Ba ke kaɗai ba ce,
Akwai dubbunai waɗanda aka raunata.

A gaɓɓai, a zuciyoyi da ma ruhikansu,
Wasu ma duka a lokaci ɗaya kamar ke dai Kandalata.

Ki yafe Mani—
Ni ma na kuskaranta.

Na yi shiru kan ki,
Tamkar ba ke ba ce zuciyata.

Shi ya sa yau nai azamar,
Magana kan ki da fatan ki jiye ta.

A ce mutum da ƙasarsa da gidansa,
A samu mutanen da suka haketa?

Mutum da ƙasarsa,
Ba shi da ƴancin ya je gonarsa domin ya nometa?

Mutum ba zai iya shagali ba,
Sai a ce an kuskaranta?

Mutum ba zai iya tafiya cikin kwanciyar hankali ba
Ba tare da zulumi da tsoro sun shiga sun fita?

Mutum ba zai iya faɗar gaskiya ba,
Sai a turo masa da mahukunta?

Mahukuntan da ya kamata su kiyaye doka,
Sune a yau da su ake lalatata?

Sarakunan mu kamar ba su,
Masu maganar ma sun dainata.

A yau mu ne kuwa taron tsintsiya a barbaje,
Da alamar, da jam'iyar ma ya nuna ta.

Kan mu a rabe kullum da safe,
Sai magana ba ma ma kiran sunanta.

Wai yaushe ne za mu duba,
Sannan muyi nazari mu hankalta.

Makiyanmu mun sansu,
Ɓerayen ofis ake shelanta.

Su ne masu wawure asusu,
Su wawure komai har ma su ƙonata.

Su yi bidiri da ƴaƴayen su,
Mu kuwa muna azabta.

Su watsa mana ƴar tsaba,
Mu biye masu suyi ta ɓeranta.

Muna bin su da sowa,
Su kuwa suyi ta ƙara wa kansu wadata.

A yau babu asibiti mai inganci,
Masu ciki kullum na azabta.

Babu hanyar titi,
Akwai garuruwan da ba a iya ƙetarata.

Babu makarantu,
Ƴaƴayanmu turancin ma ba sa iya ta.

Rayuwar mu kullum cikin ƙunci da ƙaskanci,
Saboda ƴaniska ƙalilan da ke ribata.

Mutane mu hankalta,
Ku tuna fa da Kandalata!

03/05/25

Mamako

     Kamar kullum, Kano ta tashi da zafi—zafin juma’a. Amma maimakon ta ci gaba da taku kamar yadda ta saba, sai ta jirkita daga gwadaben ga...