Showing posts with label Prose Poetry. Show all posts
Showing posts with label Prose Poetry. Show all posts

Saturday, 17 May 2025

Gare Ki

Wannan saƙo ne da na daɗe ina ta dakon sa. Yau shekaru sama da huɗu kenan rabon da na yi tozali dake, amma a kullum ruhina da ke yake tashi daga barci. Ki na nan sarkafe abin ki. Kina yadda kike so rabin rai. Jiya na jiyo a radio a na ta zabga muhawara kan maza masu kuka, sai dai na murmusa kawai. Ba na ce ba ki taɓa ganin kuka na ba. Kin sha ganinsa, tunda tare muka taso. Ranar da aka haifi ni ma ai kin gani. Amma duk ruwan hawayen da kika gani basa ɗauke da ƙunci sannan basu da ɗaci. Kawai dai ruwan hawaye ne. Ina da yaƙinin cewa kin gani a ranar da muka yi bankwana. Kin ga ruwan ƙwalla na. To amma, wasu lokutan idan na tuna da cewa mutanen da ke zagaye da ni da ɗan dama, sai naji akwai yiwuwar ba ki gane ni ba; ina can ƙurya ko kuma ɗaka, ina ɗauke da hankici ne ko tsumma, bana ce ba nima. Ban iya tunawa ba... Yanzu dai zan ƙaddara cewa baki taɓa ganin ruwan hawayena mai ɗauke da: ƙunci, da-na-sani, kewa, bege, da so ba. 

Abin da kuwa ma ba ki sani ba shine, wannan ne lokaci na ƙarshe da irin wannan hawaye ya tsatso daga gulbin idanuwana. A duk lokacin da na ji ƙwalla na kan so na ji ya ya yake. Kamar kullum dai babu komai a cikinsa. Ba shi da bambanci da ruwan sha. Ruwan rijiya. Kai hatta ma garɗinsa babu wasu ta’ajibbai da ke kewaye da shi. Hakan kuwa yasa ma na daina kukan. Saboda na san koda na yi sa, ba ya ɗauke da wannan garɗin. Wannan ɗanɗanon da na taɓa riska.

Sahiba, kin tafi da wani ɓari na rayuwata da babu mahalukin da zai iya kawo madadinsa. Ƙunci wani abu ne mai ɗaci, amma ya zauna a wani lungu a ruhina ya yi min kane-kane. A ɓoye yake mulkinsa, ta hanyar amfani da wasu shauƙin can daban wajen isar da saƙon sa. Misali, yanzu sai na ji farin ciki ya mamaye ni haka kurum, idan ko nai ƙuri, sai na ga ashe ba farin cikin kaɗai nake ba — shi ne kaɗai ya bayyana; akwai wani abu mai duhun launi a can ƙurya a zaune yana mai kallona, yana murmushi tare da gyaɗa kansa. 

Na kan ji wani ƙara a cikin ruhina wasu lokutan, koda na duba, sai na ga tana fitowa ne daga wani saƙo a can cikin ruhina. Ƙarar dai ba ta da ƙara. Shiru ce ma. Kawai tsabagen shiru ne ya sanya ƙarar fitowa. Wato dai a can cikina akwai wani irin rami kamar holoƙo da babu komai a cikinsa sai shiru. Ban ma ziyarar sa saboda tsoro da fargabar abin da zan buɗe na gani. E, ƙwarai, ni matsoraci ne, ban son ziyarar in da zai kai ni kushewa. Har yanzu ina da muradai da burika dana ke fatan cimmawa, watarana. Na san idan na shiga wannan rami kam da matsala. Ina gujewa matsala duk da yake dai ba zana iya guje masa ba, sahiba. Wannan ramin kushewarmu ne, a nan na binne soyayyarmu. A nan nake fata wata rana kurwata zata shige dan ta sadu dake.

Sai dai kuma ina rayuwa tamkar ba kya tare dani; tamkar babu ɓurɓushinki a komai na; tamkar iskar da nake shaƙa iska ce kawai, ba sinadaran hazon ruhinki ba; tamkar zuciyata na ci gaba da bugawa ne ba tare da taimakonki ba; tamkar rayuwata — a yanzu — ba wanzuwa take a doron tunaninki ba. Tamkar ba ki, sai dai kuma akwai ki a komai na, Sahiba. Tamkar ba ki, sai dai a duk sanda na tuna wane ni — mantawa nake wasu lokutan — ina ganin ki a samana kina mai kallona. 

Wannan abun, wani lokaci, na ci min rai ƙwarai amma da zaran na tuna cewa duk abubuwan da na lassafta a baya, kina da tasiri a gare su, kuma gaskiya ne, ke ɗin ce sinadarin rayuwata, sai na ji sanyi a ruhina. Sanyin na zuwa ne daga gun ki sahiba. Ai da ma kece mai sanyaya mini zuciya. 

A duk lokacin da na yi koda tunanin cewa kina nesa dani sai ruhina ya gargaɗe ni, domin wai zunubi ne mai girma faɗin haka. Wai kina kusa dani fiye da kusancin jijiyoyi ga ɗan Adam. Kuma haka ne fa, ko? Tunda dai ina tunawa da ke a duk sakan da duk minti. Barci ne kawai ke hanani tunawa dake, kuma ai wasu lokutan ina mafarkinki: wai gamu a wani dausayi; ni dake, da ƙaunar mu, muna masu kallon ruhikan mu ba tare da magana ba, akwai murmushi a saman fuskar mu sannan akwai alamar cikar aminci a kowannenmu. Ina sonki, sahiba. Ina tsananin kewarki. 

A nan alƙalamina — da na sato — ya ƙare daƙushewa, kin fini sanin iya adadin kewarki da nake yi. Kin fini sanin iya nauyin begenki da ke a ruhina. Kin fini sanin cewa ina sonki. Saboda haka, wannan rubutun duk domin ni na yi shi. Ke fa ba kya buƙatar sa — kina ganin gaskiya a can inda kike, saboda haka, kin fini sani. 


April,2024

Friday, 25 April 2025

Kukan Kurciya

Akwai wata kurciya da ke zuwa bakin tagata kullum da safiya. Kukanta mai daɗi ke tayar dani daga barci. Na kan kwashi lokaci mai tsayi ina kallonta, ina sauraran kukanta, ina mai ninkaya cikin duniyar mafarkaina wasu lokutan, har da mafarkanta— idan naci sa'a. A cikin duniyar tata mafarkai ne a jere da burika irin tasu ta dabbobi, kar ka tambaye ni wai ashe suna da mafarkai. Ca akai kai kaɗai ne mai iya yin su? 

Ƴar alkawari. Da hakan nake kiranta. Baiwar Allāh abar kwatance. A duniyar tata akwai ma'adanar rayuwarta ta baya. Nan na leƙa wata rana. Sai na ganni a wani kufayi; kango mai haske abin haskakawa. Na gano iyayen ta da ma ƴanuwanta su su duka a zaune. Bayani ne kan yadda rayuwarsu ta ke kasancewa a wannan duniyar. Mahaifin ne ke magana yanzu; baƙi, ƙaƙkaura, idanunsa ja tamkar na Hasbiya. Ya na riƙe da ƴar sanda, alamar tsufa. 

“Iyayen mu sun shaida mana cewa; an shaida wa iyayen su cewa; kakanninsu sun taɓa riskar wani zamani mai ƙayatarwa. A lokacin babu injina ballantana motoci. Saboda haka akwai bishiyoyi da dama, inda ahalinmu ke rayuwa. Rayuwa ce mai sauki a lokacin; babu ƙara, babu datti, babu shara, babu kiɗa; sannan kuma akwai gida. A kowane lokaci suna iya komawa gida ba tare da sun shiga cikin taskar wasi-wasin kasancewar yana nan ko akasinsa ba. Lokacin fa ba a cire masu bishiyu ba bisa ka'ida ba. Kamar na taɓa jiyo kakana Alto yana cewa lokacin Hausawa ke mulkin ƙasar Hausa ba Fulani ba. Sai dai ban san takamaiman lokacin wani sarki ne ba. Ku faɗa mini yarana: shin rayuwa bata fi sauki a da ba. Yanzu ko da ba a cire bishiyoyin ba, ruwan saman mai ƙarfi da ake yi zai cire shi. Duk saboda halayyar bil'adaman dake zamanin mu.”.                                   

Sai mahaifiyar tai caraf ta ƙara da cewar: 

“Ai ko jiya sai da leda ta sarkafe ƙafafuwan Lami da taje farautar ƙwari. Da ƙyar na samu na iya cirewa. Kalli har yanzu da sauranta a cikin yatsunta. Har sai lokacin da Allah ya yi. Abin da ba su ma ganewa— wato su bil'adaman nan— shi ne: abubuwan nan sun ma fi cutar su. Jiya nake ji, a tagar Mallam Sani, wai ga-baki-ɗaya makwararar Jakara ta toshe, saboda haka, mazauna kusa da ita su kiyaye, kasancewar idan aka yi ruwa mai ƙarfi, za a iya ambaliya. Ko-ko ma zafin nan da ake ta zabgawa, ko mu nan da-ba-dan tsarin hallitar da Ubangiji Ya yi mana ba, ai da wani zancen ake. Kuma duk me yasa hakan? Rashin shuka bishiyoyin da za su ci karo, koma su daɗa, waɗanda ake cirewa, da wasu dalilan can.”

Babban ɗan, wanda ya kasance ma'abocin karance-karancen tarihi, sanye da ɗan madubinsa ya ƙara da cewa: “Kun ga kuwa rayuwa ta fi daɗi a lokacin baya. Ina-ma- ina-ma, zan iya komawa can. Na biye wa tawagar Sarkin Zazzau Muhamman Makau lokacin da aka ci ƙasar sa da yaƙi. Yana tafiya da tawagarsa ina biye masa, har su isa Abu-Ja. Nayi zamana a can. Ina ma a ce a wancan ƙarnin a ka haifemu! Ga bishiyu, ga tsaunika, ga ƙoramai, ga ruwa mai kyau. Rayuwa mai daɗi! Uwa uba, ga tsafta. Gari ƙal-ƙal sai kace Aljanna.”

Shin ya Aljanna take? Ka taɓa zuwa ne?” In ji kurciyata, wacce ta kasance a kishingiɗe a saman tsabar da ke kwance a kangon, kanta na kan fika-fikin mahaifiyarta. Sai na ga duka manyan sun ƙalƙale da dariya. Mahaifiyar ko ta janyo ta, ta lakaci hancinta da nata hancin cikin zallar so. 

Mahaifin ya yi gyarar murya ya na mai cewa: “lokaci ya yi, yanzu ina muka dosa?”. A daidai lokacin sai na jiyo ƙarar injin ‘rum-rum-rum’. Sai muka jiyo ‘dum!’ Mai ƙarfi. Na waiga, kafin na juyo kuma, sai na jiyo “Fap...fap...fap”...

Mahaifiya ke jan gora, mahaifin ke bayan ayarin, Ƴaƴayan na tsakiya. Tafiya suke kamar ba za su tafi ba . Da suka nisa sai duk suka juyo, suna masu kallon gidansu a ƙaro na ƙarshe. “Rrrr”— ƙara ya tsaya cak. Amma bishiyarsu— gidansu— babu. Sun tafi kenan. Har abadan... a-ba-da.

Da na dawo zahiriyya, sai na nitsa a cikin kogon tunani. Abubuwan da suka wakana tamkar a mafarki. Na yi mamaki ƙwarai da ba su lura dani ba. Wai shin ko na mutu ne?... Amma kuma wani abu guda daya kasance yana ta yi min kulumboto a cikin zuciyata; kamar na san wurin ko ma na taɓa rayuwa a inda na riske su. Kamar na san kangon nan. Kamar na san ginin nan. Kai, na ma san su! Da na nitsa sai na fahimci cewar, ai inda ma suke tsaye a nan ɗakina yake. Inda aka yi wa ƴaƴayan huɗuba ai a cikin gidan nan yake. Bishiyar da ma na tsakiyar kangon ne. 

Dabbobi ma, kamar ɗan Adam ba sa mance gida. Dabbar ma tsuntuwa. Tsuntsuwar ma Kurciya. Ashe, shi ya sa, a kullum take tashina daga barci. Kukan da take yi ai tuni take min, magana take min, wa'azi take yi min: “Duk inda halittar Ubangiji zai kai ya kawo ba za ya taɓa mantawa da gida ba. Nan ne gidanmu, ba zan iya mantawa da shi ba.”

Washegari na tashi a makare kasancewar ba ta zo ba. Mai tashina ba ta. Sati yazo ya wuce, wata ya rarrafa a sukwane, shekara ta zo a guje. Lokaci mai tsayi ya ja. Amma kullum da tunanin kurciyata nake tashi daga barci.

 “Baba, lokacin shan shayi yayi” na jiyo ɗan autana Sambo na faɗi. Na tashi, na shirya, na ishe su a ƙarƙashin bishiyar da na dasa shekarun baya— irin wacce na gani ne a mafarkin kurciyata. Kuma a inda na ganta a nan na kuma dasa ta. Ga kujeru, ga shayi, ga iyali, sannan ga Kurtattakina a saman bishiya, suna ta kukan su. “Kukan Kurciya dama ai jawabi ne.” ko ni ne na faɗa, ko Kurtattakin dake saman bishiyar ne, ba na ce ba.

MA. Maibasira

24/04/25





Mamako

     Kamar kullum, Kano ta tashi da zafi—zafin juma’a. Amma maimakon ta ci gaba da taku kamar yadda ta saba, sai ta jirkita daga gwadaben ga...