Showing posts with label Waƙe. Show all posts
Showing posts with label Waƙe. Show all posts

Monday, 9 June 2025

Yawon Duniya

Masoyiya, shin za ki iya shimfiɗa 
Mini tabarma a wani sashe na 
Zuciyar ki don na zamna?
 
Ƙafufuwana sun gaji da 
Taku a cikin zuciyarki 
Babu dare, babu rana.

Ba lallai sai kin samo 
Kilishi ba ko kujerar 
Nan mai taushi da laushi.

Kawai soyayyarki nake so 
Ta zame mana tabarma; 
Ni a gefe ɗaya, ke a ɗaya.

Ta ja mu, ta ɗaga mu, ta lula mu:
Mu keta gajimare; mu ratsa ta 
Gangamin tattabaru; mu wuce sinadaran
Numfashi; mu lula mu tafi can inda cida 
Ke koyan tashi. Daga nan, ƙila, 
Sai mu garzaya duniyar taurari;
Mu faɗa kogin da ke bisansu, mui wanka, 
Mu sauya buƙatu, mu kaifafa muradai;
Mu tsaftace soyayyarmu.

A cikin zuciyarki, da zaki yarda, 
Da sai na janyo tabarmar nan bakin teku. 
Mu zamana muna kallon shirgawar 
Kifaye mu kadanmu 
Sai kuma teku.

Da zaki yarda, da sai na baza 
Komata don na kamo kifayen 
Da ke cikinai, kowannensu, na 
Buɗe cikinsu, inda ƙoƙon lu'ulu'u 
Mai ɗauke da soyayyarmu 
Ke ciki a ɓoye.

Masoyiya, so nake kawai na samu 
Aminci a cikin zuciyarki; ki ɗan lasa 
Mini daga tekun ƙaunarki; ki ci gaba 
Da alkinta mana soyayyarmu a cikin 
Ƙokon lu'ulu'u nan mai haske. 
Ƙila wataran, idan muka ƙare 
Yawon duniyar mu, zamu shiga 
Domin mu ga iya girmanta. 

Wednesday, 7 May 2025

Sunayensu

Eh su, mai sunan su,
A haka aka haife su babu sunayensu?

Lokacin da kuke buƙatar kuriunsu,
Ku ne har mazaɓarsu dan ku tantancesu

Loton nan har hotunan su kuka maka,
A bango saboda kar ya wucesu.

Sai yau ɗin da ba ransu,
Saboda rashin ta ido kuka manta sunayensu?

Ina kuke lokacin da a ka kashe su,
Aka sare su sannan aka ƙona su?

Ina kuke lokacin da suke neman agaji,
Da bakunansu, babu mai kula su?

Ina kuke lokacin da aka ciri ɗaya daga kwata,
Aka wurga shi dan a ƙona su?

Ina kuke lokacin da fatar su yake zagwanyewa,
Ƙuna da raɗaɗin azaba na ta cin su?

Ina kuke lokacin da tsabar azaba,
Ta tayar da gaɓoɓin wasunsu?

Ina kuka ɓoye lokacin da aka fara bin,
Karnukan su da sara a na kashe su?

Ina kuka ɓoye lokacin da suke fitar da,
Hayaki daga bakunansu?

Na ce ku matsiyatan nan, marasa mutuncin nan,Masu ribatar nan, 
Ina kuke lokacin da suka rasa rayinsu?

Yau hawaye ke kwaranya a fuskata,
Zuciyata duk ta cika da raɗaɗi sanadinsu.

Akwai nauyi a ruhina a duk lokacin da na tuna da su,
Ji nake yi tamkar na ma san su.

Ban san sunayen su ba har yanzu ,
Saboda ƴaniskan sunƙi su duba su.

Na dai sanya masu suna,
Akwai Aminu akwai Ilyasu.

Da Ɗalhatu da Haruna,
Ƴan uwan juna na san su.

Ibrahima Halilu, kamili,
Ƙurani da Hadisai yana ta dakon su

Zubairu mai masoyiya zubaida,
Har yau ta kasa kallon bidiyon su.

A kullum hawaye ne ke kwaranya,
Idan har ta tuna da yadda aka ma su.

Sai ta ji kamar ma ana ƙona ta,
Idan ta tuna da soyayyarsu da Alkawarin su.

A zuciyarta wuta ke ta burtsatsowa,
Wutar bege da kewansu.

Shi kenan babu Zubairu,
Ya tafi kenan shi da ma sauransu. 

Na tuna da na cikin tayar nan,
Ɗan farin nan mai suna Harisu.

Na tuna yadda suka masa,
Yana ihu su kuwa suna dariyar su.

Ya na ta ajiyar zuciya,
Su kuwa suna ta muguntarsu.

A duk lokacin nan babu ɗaya daga cikin—
Su ƴan iskan nan da ya zo agajinsu.

Haka aka yi ta yi tsawon awanni,
Mutane fa a ƙasarsu.

Aka yi ta ƙona su ana daɓe su,
Da su da muradansu;

Abubuwan da suka so suyi,
Abubuwan ma da suke kan yi nasu.

Da masu ajiye kuɗi a cikin jaka,
Da masu ajiye shi a asusu.

Kudaɗen da za su saya wa,
Masoyansu balangu da kilishi da su.

Kayan sallah kuwa an tura kuɗi,
Yana nan yana jiransu.

Su zo su sanya sa,
Ashe babu damar ya gan su.

Iyayen da ke tagumi duk yamma,
Saboda kewar rashin ɗansu.

Ƴaƴayen da ke zaune a ƙofa,
Suna ta dakon dawawar ubansu.

Ashe ya tafi kenan,
Sai dai gawarsa za a kawo masu.

Ruhiƙa sun ƙunana,
Zuciyoyi ma da rauninsu.

A kullum da shi za su tashi,
Da safiya har zuwa barcin su.

Ƙunar rashi madauwamiya,
A kullum suna ta dakon su.

Ba fa ma rashin ba ne kaɗai,
Har da ma yadda aka zo gunsu —

Da labarin yadda,
aka daddatse jininsu.

Aka bige su, aka ƙona su,
Aka raunata su.

Akwai ƙunci da ɗacin,
Da ke daskare a wani saƙo nasu.

Haka za suyi ta dakon su,
Har ƙarshen rayuwarsu.

Mafarkai da burikan masoyansu,
Na can ƙuryar ruhikansu.

Soyayya da ƙunar rashin masoyansu,
Saboda tsabagen wauta ta mutanen ƙasarsu.

Wautar da ƴaniskan suke rurawa,
Domin biyan buƙata nasu.

Tashin tashina za ta cigaba da ɗorewa,
Har sai sun shiga taitaiyinsu.

Idan suka ƙi shiga ta lalama,
Ai sai a koya masu.

Ta hanyar fitar da su,
daga ɗakin da suke, su je can masu.

Mu koresu, 
Mu yi fatali da kayan su.

Mu ƙi yarda da duk batun su,
Ko ma wani abu da zai fito daga bakunansu.

Mu tsaya da kafar mu,
Wajen yin ball da su.

Tun da sun iya rura wutar kabilanci,
Mu Kore su, mu kakkaɓe tabarmarsu.

Mu faɗa masu ba su da matsuguni a nan,
Su tashi su yi tafiyar su.

Mu faɗa masu ƙasar ta mu,
Ba ta zamowa filin wasansu.

Da zasu dinga amfani damu,
Wajen biyan buƙatarsu.

Mu tuna masu da dubunnai,
Da aka salwantar da ransu.

Mu tuna masu da masoya biyun nan,
Da aka raba su har da soyayyarsu.

Mu tuna masu da hawayen mahaifiyar nan,
Da tagumin ƴaƴayansu.

Mu tuna masu da kwantacciyar ciwon nan,
Da ke binne a zuciyar ahalinsu.

Mu tuna masu da zaluncinsu,
Da ke rura wutar ƙiyayya duk domin su.

Mu tuna masu da soyayyar da ba a kai ga cimmawa ba,
Ƙaunar da aka rusa wa wasunsu.

Mu tuna masu da komai,
Komai har da furfurar wasunsu.

Kar mu bar su,
Kar mu sake su.

Idan suna guduwa,
Mu taɗe su, mu ingiza su!

Su rasa sukuni a yankin su,
Har sai sun tuna da sunayensu.

Monday, 5 May 2025

Kandalata

From Pinterest
Baza na yabe su ba,
Su waɗannan da suka sace mini kuriciyata.

Baza na je gun su ba,
Su dai masu sace mini dukiyata.

Baza na kula su ba,
Su waɗancan masu zaluntata.

Duk da hakan ba zai hana ni faɗa ba,
Kan yadda suke gudanar da ƙasata.

A yau babu walwala ta zahiri,
Ta tunanin ma babu ita.

Babu sukunin yin barci,
Babu sukunin yin mata.

Abinci ya wahala,
Magidanta sai dai su kwatanta.

Ga su can a ofis,
Suna can suna ribatata.

Suyi ado da ƙawa,
A ce ga Kapasiti suna bazata.

Ƙwalwar su a doɗe,
Ba Arabin, Bokon ma da ƙyar a ka sha ta.

Ba su san komai ba a harkar mulki 
sai dai nuna Bajinta—

Wajen zalunci kan marasa galihu,
Ga ƙasa nan sun ƙi su gyarata.

Komai na ƙasar ya lalace,
Mu kaɗai ya rage su lalata!

Mutum da rigar sa da a cike,
Yau shi ke yawo a cikinta.

A yau ƙiriniya babu ita,
Yara sun dena ta-ta-ta.

Daga sun taso,
Sai dai a jibga masu shirgi dan suje ƙolanta.

Makarantu sun rufeta,
Mallamai duk sun jigata.

Masana'antunmu ma na gida,
Duk an bi an gurgunta.

Dan talaka ba shi ba shinkafa,
Sai dai tsabar da zai iya kwatanta.

Iyaye sai zulumi,
Ƴaƴaye kuwa sai dai su ƙarata.

Dan Babu ma gonar,
Da za su je su nomata.

Idan sun tafi ma,
Babu tabbacin zasu iya komai ma a kanta—

Sai sun biya haraji,
Ko kuwa a ƙonata.

Ƴan bindiga daɗi,
Na cin kariyar su batare da sun babbakata.

Manyan mu na yawo,
Da tsaro domin su tsereta.

Fyaɗe, ƙwace, kisa,
Sun addabi ƙasata.

Har na tuna da wata yarinya,
A can saman tsauni, Kandalata.

Ta kan shigo cikin Gari duk sati 
domin ta sai da furarta.

Da shi ta ke ƙoƙarin,
Ciyar da ahalinta.

Bom ɗin wajen mauludi,
Ya kashe mahaifinta, ya raunata uwarta.

A kullum da ka kalleta,
Sai ka ji zuciyarka ta raunata.

Na tuna da yadda,
Su ƴan iskan suka ishe ta.

Suka kama uwarta,
Ita ma kandala suka kamota.

Suka afka mata—
A gaban uwarta.

Babu ƙwalla ko guda,
Idan ka kalli idaniyarta.

Akwai zulumi da tsana,
A can cikin zuciyarta—

Sun kwanta ruf,
Ita ma hakanta.

Kandalata dake zuwa gaɗa,
Ƴar yarinya ƙarama dake wasanta.

Yau babu ita,
Sai dai ƙoƙonta.

Ta shige cikinta,
Ta yi ruf, ta rufe abinta.

Kandalata da ke son ta zama likita,
Yau da wuya ma kaga fitarta.

Mahaifiyarta ma wacce ta ke gani,
Ta haɗiyi zuciya ta barta.

Yau ƙasar ta da ta ke kishi,
Ta yarda aka hainceta.

Babu wanda ya zo agajinta,
Babu ma mai kallon ta.

Ita kaɗanta,
ke ta dakon kayanta;

Ƙunar rai da,
Azabar zuciyarta.

Ta kan kalli rana,
Da yamma daga tagarta.

Ta kan kwatanta
rayuwarta da ranarta.

Sai dai ita ba ta zuwa ko'ina,
Daga ɗaki sai gadonta.

Ilimi babu shi,
Aikin ma ba ta.

Kandalata ba ta,
Ta ɓace ɓat a duniyarta.

Wannan yarinyar da na sani,
A kullum tana cikin murmushinta.

Yau a halin da take,
Babu ita babu murmushinta.

Ga su can a ofis,
Suna ta harkokinsu babu ita—

A zancen su, da kalaman bakinsu,
Ba sa ko furtata.

Al'ummarmu sun mance da ita,
Kowa ma yayi kamar babu ita.

Kandalata ta rufe ƙofar rayuwarta,
Ta tsani alummarta.

Wani lokacin har tsanar,
Na gangarowa ƙuncinta.

Ta hanyar hawaye,
Da ke zirya a saman fuskarta.

Ta kan tunano rayuwarta—
Ta baya da raunin zuciyarta.

Ta kan tuna da raɗadin da ke,
Binne a birnin zuciyarta—

A duk sakan da minti,
Dake motsi a rayuwarta.

O ni Kandalata!
Labarin ki akwai zafi ƙwarai na hankalta.

Ba ke kaɗai ba ce,
Akwai dubbunai waɗanda aka raunata.

A gaɓɓai, a zuciyoyi da ma ruhikansu,
Wasu ma duka a lokaci ɗaya kamar ke dai Kandalata.

Ki yafe Mani—
Ni ma na kuskaranta.

Na yi shiru kan ki,
Tamkar ba ke ba ce zuciyata.

Shi ya sa yau nai azamar,
Magana kan ki da fatan ki jiye ta.

A ce mutum da ƙasarsa da gidansa,
A samu mutanen da suka haketa?

Mutum da ƙasarsa,
Ba shi da ƴancin ya je gonarsa domin ya nometa?

Mutum ba zai iya shagali ba,
Sai a ce an kuskaranta?

Mutum ba zai iya tafiya cikin kwanciyar hankali ba
Ba tare da zulumi da tsoro sun shiga sun fita?

Mutum ba zai iya faɗar gaskiya ba,
Sai a turo masa da mahukunta?

Mahukuntan da ya kamata su kiyaye doka,
Sune a yau da su ake lalatata?

Sarakunan mu kamar ba su,
Masu maganar ma sun dainata.

A yau mu ne kuwa taron tsintsiya a barbaje,
Da alamar, da jam'iyar ma ya nuna ta.

Kan mu a rabe kullum da safe,
Sai magana ba ma ma kiran sunanta.

Wai yaushe ne za mu duba,
Sannan muyi nazari mu hankalta.

Makiyanmu mun sansu,
Ɓerayen ofis ake shelanta.

Su ne masu wawure asusu,
Su wawure komai har ma su ƙonata.

Su yi bidiri da ƴaƴayen su,
Mu kuwa muna azabta.

Su watsa mana ƴar tsaba,
Mu biye masu suyi ta ɓeranta.

Muna bin su da sowa,
Su kuwa suyi ta ƙara wa kansu wadata.

A yau babu asibiti mai inganci,
Masu ciki kullum na azabta.

Babu hanyar titi,
Akwai garuruwan da ba a iya ƙetarata.

Babu makarantu,
Ƴaƴayanmu turancin ma ba sa iya ta.

Rayuwar mu kullum cikin ƙunci da ƙaskanci,
Saboda ƴaniska ƙalilan da ke ribata.

Mutane mu hankalta,
Ku tuna fa da Kandalata!

03/05/25

Da Kuma Akwai Wannan Lumanar Da Ba Za A Iya Fasalta Wa Ba

Da akwai wannan lumanar da bawa kan riska yayin da ya tsinci wannan littafin da ya yi shekaru yana nema a wata ƙurya a cikin ma'adanar t...