Eh su, mai sunan su,
A haka aka haife su babu sunayensu?
A haka aka haife su babu sunayensu?
Lokacin da kuke buƙatar kuriunsu,
Ku ne har mazaɓarsu dan ku tantancesu
Loton nan har hotunan su kuka maka,
A bango saboda kar ya wucesu.
Sai yau ɗin da ba ransu,
Saboda rashin ta ido kuka manta sunayensu?
Ina kuke lokacin da a ka kashe su,
Aka sare su sannan aka ƙona su?
Ina kuke lokacin da suke neman agaji,
Da bakunansu, babu mai kula su?
Ina kuke lokacin da aka ciri ɗaya daga kwata,
Aka wurga shi dan a ƙona su?
Ina kuke lokacin da fatar su yake zagwanyewa,
Ƙuna da raɗaɗin azaba na ta cin su?
Ina kuke lokacin da tsabar azaba,
Ta tayar da gaɓoɓin wasunsu?
Ina kuka ɓoye lokacin da aka fara bin,
Karnukan su da sara a na kashe su?
Karnukan su da sara a na kashe su?
Ina kuka ɓoye lokacin da suke fitar da,
Hayaki daga bakunansu?
Na ce ku matsiyatan nan, marasa mutuncin nan,Masu ribatar nan,
Ina kuke lokacin da suka rasa rayinsu?
Yau hawaye ke kwaranya a fuskata,
Zuciyata duk ta cika da raɗaɗi sanadinsu.
Akwai nauyi a ruhina a duk lokacin da na tuna da su,
Ji nake yi tamkar na ma san su.
Ban san sunayen su ba har yanzu ,
Saboda ƴaniskan sunƙi su duba su.
Na dai sanya masu suna,
Akwai Aminu akwai Ilyasu.
Da Ɗalhatu da Haruna,
Ƴan uwan juna na san su.
Ibrahima Halilu, kamili,
Ƙurani da Hadisai yana ta dakon su
Zubairu mai masoyiya zubaida,
Har yau ta kasa kallon bidiyon su.
A kullum hawaye ne ke kwaranya,
Idan har ta tuna da yadda aka ma su.
Sai ta ji kamar ma ana ƙona ta,
Idan ta tuna da soyayyarsu da Alkawarin su.
A zuciyarta wuta ke ta burtsatsowa,
Wutar bege da kewansu.
Shi kenan babu Zubairu,
Ya tafi kenan shi da ma sauransu.
Na tuna da na cikin tayar nan,
Ɗan farin nan mai suna Harisu.
Na tuna yadda suka masa,
Yana ihu su kuwa suna dariyar su.
Ya na ta ajiyar zuciya,
Su kuwa suna ta muguntarsu.
A duk lokacin nan babu ɗaya daga cikin—
Su ƴan iskan nan da ya zo agajinsu.
Haka aka yi ta yi tsawon awanni,
Mutane fa a ƙasarsu.
Aka yi ta ƙona su ana daɓe su,
Da su da muradansu;
Abubuwan da suka so suyi,
Abubuwan ma da suke kan yi nasu.
Da masu ajiye kuɗi a cikin jaka,
Da masu ajiye shi a asusu.
Kudaɗen da za su saya wa,
Masoyansu balangu da kilishi da su.
Masoyansu balangu da kilishi da su.
Kayan sallah kuwa an tura kuɗi,
Yana nan yana jiransu.
Su zo su sanya sa,
Ashe babu damar ya gan su.
Iyayen da ke tagumi duk yamma,
Saboda kewar rashin ɗansu.
Ƴaƴayen da ke zaune a ƙofa,
Suna ta dakon dawawar ubansu.
Ashe ya tafi kenan,
Sai dai gawarsa za a kawo masu.
Ruhiƙa sun ƙunana,
Zuciyoyi ma da rauninsu.
A kullum da shi za su tashi,
Da safiya har zuwa barcin su.
Ƙunar rashi madauwamiya,
A kullum suna ta dakon su.
Ba fa ma rashin ba ne kaɗai,
Har da ma yadda aka zo gunsu —
Da labarin yadda,
aka daddatse jininsu.
Aka bige su, aka ƙona su,
Aka raunata su.
Akwai ƙunci da ɗacin,
Da ke daskare a wani saƙo nasu.
Haka za suyi ta dakon su,
Har ƙarshen rayuwarsu.
Mafarkai da burikan masoyansu,
Na can ƙuryar ruhikansu.
Soyayya da ƙunar rashin masoyansu,
Saboda tsabagen wauta ta mutanen ƙasarsu.
Wautar da ƴaniskan suke rurawa,
Domin biyan buƙata nasu.
Tashin tashina za ta cigaba da ɗorewa,
Har sai sun shiga taitaiyinsu.
Idan suka ƙi shiga ta lalama,
Ai sai a koya masu.
Ta hanyar fitar da su,
daga ɗakin da suke, su je can masu.
Mu koresu,
Mu yi fatali da kayan su.
Mu ƙi yarda da duk batun su,
Ko ma wani abu da zai fito daga bakunansu.
Mu tsaya da kafar mu,
Wajen yin ball da su.
Tun da sun iya rura wutar kabilanci,
Mu Kore su, mu kakkaɓe tabarmarsu.
Mu faɗa masu ba su da matsuguni a nan,
Su tashi su yi tafiyar su.
Mu faɗa masu ƙasar ta mu,
Ba ta zamowa filin wasansu.
Da zasu dinga amfani damu,
Wajen biyan buƙatarsu.
Mu tuna masu da dubunnai,
Da aka salwantar da ransu.
Mu tuna masu da masoya biyun nan,
Da aka raba su har da soyayyarsu.
Mu tuna masu da hawayen mahaifiyar nan,
Da tagumin ƴaƴayansu.
Mu tuna masu da kwantacciyar ciwon nan,
Da ke binne a zuciyar ahalinsu.
Mu tuna masu da zaluncinsu,
Da ke rura wutar ƙiyayya duk domin su.
Mu tuna masu da soyayyar da ba a kai ga cimmawa ba,
Ƙaunar da aka rusa wa wasunsu.
Mu tuna masu da komai,
Komai har da furfurar wasunsu.
Kar mu bar su,
Kar mu sake su.
Idan suna guduwa,
Mu taɗe su, mu ingiza su!
Su rasa sukuni a yankin su,
Har sai sun tuna da sunayensu.
No comments:
Post a Comment