Lokaci kaɗan sai hasken makomar wannan ƙasa ya baɗe mini ɗakina. Lokaci guda kuma sai ya janye, ya daina kwaranya a dausayina. Ƙasar nan tamu ce, ita kaɗai ce gare mu, amma a yau na kasa shaida ta; na kasa gane kalar mayafinta. Wasu daga cikin ƴaƴanta na dunkule shara a hannu, su watsa ai ta rububinta. Su damtse mana yatsu, su mika mana azurfa mu yi ta yabonsu. Yau sukuni ya yi ɓatan dabo a sarari ya koma can inda rana ta kwanta. Yau babu mai kallon kwanciyar rana ballantana ma ya yi tunanin sukuninsa — da ke can tare da rana, yana dakon komowar sa.
Haske yakan tuna mini da ƙauna, duhu kuma ya kusanto ni ga wutarta. Haske da duhu na tasaruffi a zuciya, su suka turniƙe sararinta. Yaushe za mu samu sukuni a can sadarin rana to? Yaushe duk abubban za su rikiɗe ya zam hadarin ya kau? Yaushe ruwan za shi sauko; ƙasa ta fid da ƴaƴanta? Ƴaƴaye kyawawa masu yabanyar zaman lafiya. Yaushe ne makomarmu za ta haska ta bayyana mana da lambunta? Da ke ɗauke da shukoki iri-iri masu kalar lumana?
Ƙasar nan da zafi da ƙunci. Sannan an ƙi ba mu mafaici. Idan muka je nema sai fa maɗaci. An damƙe mu an barmu da ƙirci. Ƙasar nan da ƙuna a ƙalbi, ƴaƴanta ba su da sukuni, zuciyoyin kowanensu da rauni, da ke shiga har cikin rai yai mulki.
Bishiyar Gamjin ta fara mutuwa, rassanta na ta bushewa. Mikiyoyin na ta rage yawa. Zakunan ga su a na ta bindigewa. Taurari mahaskaka suna ta rage yawa. Hayaƙin ƙunci a ko'ina na turniƙewa. Amma, har yanzu, rana na fitowa: hadari na haɗuwa, iskar hunturu na kaɗawa, yayyafi na saukowa (a hankali amma).
Duk da yake kududdufin ya kusa bushewa, rijiyar na ci gaba da cika da batsewa. Duk da yake hasken na janyewa, akwai ranar da za ta kuma dawowa. Duk da yake malam-buɗe-littafi na ta ɓacewa, akwai tsuntsayen da ke shilgawa. Duk da yake gangar ta kuma fashewa, kiɗar na fa canza wa. Duk da yake duk abubban da nake ta faɗa hasashe ne, ba a raba ɗan Adam da wassafawa! Saboda ƙasar nan dai ita kaɗai gare mu, ba mu iya sauyawa. Saboda ƙamshin turarenta a jikkunanmu ba shi taɓa nasuwa. Saboda bugun zuciyarmu na tafiya ne a bisa tsarin wannan uwa. Saboda a duk sanda muka tsinci kanmu a rana ita ce ke zame mana inuwa. Saboda ko ina aka binne mu, ƙarshe ruhinmu shigifarta zai kuma dawowa. Saboda ita ce mafari kuma ita ce kushewa! Saboda ko ina za mu, alƙiblarmu na a gidan wannan tauraruwa.
Idan muka ɓace a saharar rayuwa, ita ce za ta nuna mana hanya mafi karɓuwa. Idan muka gaza samun ruwa a saharar, ita ce za ta zo ta yi mana ban ruwa. Ita ce mafakar matafiyi idan ya ya yi nitso a ƙangin damuwa. Ita ce mai ceton sa idan ya dulmiye ya kasa fitowa. Wannan ƙasa ce komai, kun ga dole matafiyi ya ci gaba da tarairayar wannan uwa.
Haske za ya iya dawowa, duhun zai iya yayewa — tamkar giza-gizan da hannu ba ya iya taɓowa, tamkar murjanan kalmomin da ke da daɗin furtawa, tamkar sanyayyar iskar asubahin da ke sanya annashuwa. Tamkar... Tamkar... Tamkar ita. Ita ɗin dai wannan uwa!
Alhassan Maibasira
11/08/25
Haske yakan tuna mini da ƙauna, duhu kuma ya kusanto ni ga wutarta. Haske da duhu na tasaruffi a zuciya, su suka turniƙe sararinta. Yaushe za mu samu sukuni a can sadarin rana to? Yaushe duk abubban za su rikiɗe ya zam hadarin ya kau? Yaushe ruwan za shi sauko; ƙasa ta fid da ƴaƴanta? Ƴaƴaye kyawawa masu yabanyar zaman lafiya. Yaushe ne makomarmu za ta haska ta bayyana mana da lambunta? Da ke ɗauke da shukoki iri-iri masu kalar lumana?
Ƙasar nan da zafi da ƙunci. Sannan an ƙi ba mu mafaici. Idan muka je nema sai fa maɗaci. An damƙe mu an barmu da ƙirci. Ƙasar nan da ƙuna a ƙalbi, ƴaƴanta ba su da sukuni, zuciyoyin kowanensu da rauni, da ke shiga har cikin rai yai mulki.
Bishiyar Gamjin ta fara mutuwa, rassanta na ta bushewa. Mikiyoyin na ta rage yawa. Zakunan ga su a na ta bindigewa. Taurari mahaskaka suna ta rage yawa. Hayaƙin ƙunci a ko'ina na turniƙewa. Amma, har yanzu, rana na fitowa: hadari na haɗuwa, iskar hunturu na kaɗawa, yayyafi na saukowa (a hankali amma).
Duk da yake kududdufin ya kusa bushewa, rijiyar na ci gaba da cika da batsewa. Duk da yake hasken na janyewa, akwai ranar da za ta kuma dawowa. Duk da yake malam-buɗe-littafi na ta ɓacewa, akwai tsuntsayen da ke shilgawa. Duk da yake gangar ta kuma fashewa, kiɗar na fa canza wa. Duk da yake duk abubban da nake ta faɗa hasashe ne, ba a raba ɗan Adam da wassafawa! Saboda ƙasar nan dai ita kaɗai gare mu, ba mu iya sauyawa. Saboda ƙamshin turarenta a jikkunanmu ba shi taɓa nasuwa. Saboda bugun zuciyarmu na tafiya ne a bisa tsarin wannan uwa. Saboda a duk sanda muka tsinci kanmu a rana ita ce ke zame mana inuwa. Saboda ko ina aka binne mu, ƙarshe ruhinmu shigifarta zai kuma dawowa. Saboda ita ce mafari kuma ita ce kushewa! Saboda ko ina za mu, alƙiblarmu na a gidan wannan tauraruwa.
Idan muka ɓace a saharar rayuwa, ita ce za ta nuna mana hanya mafi karɓuwa. Idan muka gaza samun ruwa a saharar, ita ce za ta zo ta yi mana ban ruwa. Ita ce mafakar matafiyi idan ya ya yi nitso a ƙangin damuwa. Ita ce mai ceton sa idan ya dulmiye ya kasa fitowa. Wannan ƙasa ce komai, kun ga dole matafiyi ya ci gaba da tarairayar wannan uwa.
Haske za ya iya dawowa, duhun zai iya yayewa — tamkar giza-gizan da hannu ba ya iya taɓowa, tamkar murjanan kalmomin da ke da daɗin furtawa, tamkar sanyayyar iskar asubahin da ke sanya annashuwa. Tamkar... Tamkar... Tamkar ita. Ita ɗin dai wannan uwa!
Alhassan Maibasira
11/08/25

No comments:
Post a Comment