A halittun Ubangiji akwai wadanda ban sani ba
Wadanda muka sani ba mu sani ba
Da wandanda ba mu sani ba
Kuma ba za mu taɓa sani ba
Kamar dai itaciyar nan da ban sani ba
Ga ta a tsaye ƙiƙam tana rausayawa
Ga furanninta, ɗoraye, na karkadawa
Ga ƙamshin ganyayenta na mamayewa
Ga kaɗawar rassanta na ƙayatarwa
Ga fatsin-fatsin rana na ta ratsowa
Ga tsuntsaye ta ko’ina na ta wilkitawa
Ga daddaɗar sautinsu mai dulmiyarwa
Ita wannan itaciya da ban sani ba
Ta ciyar da ni daga dausayinta ba ta sani ba
Na cika maƙil har na nemo taskar alkintawa
Ita wannan yar itaciyar da ban sani ba
Furanninta kyawawa sun yaɗo a farfajiyar zuciya
Ban santa ba. Bai kuma zama lallai na san ta ba
Nan da wasu daƙiƙu ma ba lallai na tuna ta ba
Ba sai mun san juna ba za mu yi musayar taskar kauna
Ba sai mun fahimci juna ba za mu so juna
Ba sai ta tsam mini daga ƴaƴanta ba zan yabe ta
Ba sai na yi mata ban ruwa ba za ta ƙaunace ni
Ba sai launukan sun zam ɗaya ba za mui so da ƙauna
Ba sai kamanni da zanen fuska sun zam daya ba
Ba sai muna iya gane zantukan juna ba ma
Kalolin bakan gizo ba sa gwaraye juna ai
Kuma hakan ba ya hana su rike hannun juna
A halittun ubangiji akwai wandanda ban sani ba
Amma, duk da ban san su ba
A ruhina, akwai wannan son da na ajiye domin su
Duk da ba su san ni ba, ba su kuma san
Da wannan ajiyayyar son ba
Alhassan Maibasira
08/12/25
No comments:
Post a Comment